< Deuteronômio 33 >

1 Esta, porém, é a benção com que Moisés, homem de Deus, abençoou os filhos de Israel antes da sua morte
Wannan ita ce albarkar da Musa mutumin Allah ya furta a kan Isra’ilawa, kafin yă rasu.
2 Disse pois: O Senhor veio de Sinai, e lhes subiu de Seir; resplandeceu desde o monte Paran, e veio com dez milhares de santos: à sua direita havia para eles o fogo da lei.
Ya ce, “Ubangiji ya zo daga Sinai ya haskaka a bisansu daga Seyir; ya haskaka daga Dutsen Faran. Ya zo tare da dubban tsarkakansa daga kudu, daga gangara dutsensa.
3 Na verdade ama os povos; todos os seus santos estão na tua mão; postos serão no meio, entre os teus pés, cada um receberá das tuas palavras.
Tabbatacce kai ne wanda yake ƙaunar mutane; dukan tsarkaka suna a hannunka. A ƙafafunka, duk suka rusuna, daga wurinka kuma suka karɓi umarni,
4 Moisés nos deu a lei por herança da congregação de Jacob.
dokar Musa ta ba mu dokoki, mallakar taron Yaƙub.
5 E foi rei em Jeshurun, quando se congregaram em um os Cabeças do povo com as tribos de Israel.
Shi ne sarki a bisa Yeshurun sa’ad da shugabannin mutane suka taru, tare da kabilan Isra’ila.
6 Viva Ruben, e não morra, e que os seus homens sejam numerosos.
“Bari Ruben yă rayu, kada yă mutu, kada mutanensa su zama kaɗan.”
7 E isto é o que disse de Judá; e disse: Ouve, ó Senhor, a voz de Judá, e introduze-o no seu povo: as suas mãos lhe bastem, e tu lhe sejas em ajuda contra os seus inimigos.
Ya kuma faɗa wannan game da Yahuda, “Ka ji, ya Ubangiji, kukan Yahuda; ka kawo shi wurin mutanensa. Da hannuwansa ya kāre kansa. Ka taimake shi a kan maƙiyansa!”
8 E de Levi disse: Teu tumim e teu Urim são para o teu amado, que tu provaste em Massah, com quem contendeste às águas de Meribah.
Game da Lawi ya ce, “Tummim da Urim na mutumin da ka nuna masa tagomashi ne. Ka gwada shi a Massa; ka yi faɗa da shi a ruwan Meriba.
9 Aquele que disse a seu pai e a sua mãe: Nunca o vi; e não conheceu a seus irmãos, e não estimou a seus filhos: pois guardaram a tua palavra e observaram o teu concerto.
Ya yi zancen mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, ‘Ban kula da su ba.’ Bai gane da’yan’uwansa ba, ko yă yarda da’ya’yansa, amma ya kiyaye maganarka ya tsare alkawarinka.
10 Ensinaram os teus juízos a Jacob, e a tua lei a Israel; meteram incenso no teu nariz, e o holocausto sobre o teu altar.
Ya koyar da farillanka ga Yaƙub, dokarka kuma ga Isra’ila. Ya miƙa turare a gabanka da kuma hadaya ta ƙonawa ɗungum a kan bagadenka.
11 Abençoa o seu poder, ó Senhor, e a obra das suas mãos te aguarde: fere os lombos dos que se levantam contra ele e o aborrecem, que nunca mais se levantem.
Ka albarkaci ɗaukan dabarunsa, ya Ubangiji, ka kuma ji daɗin aikin hannuwansa. Ka murƙushe kwankwaso waɗanda suka tayar masa; ka bugi abokan gābansa har sai ba su ƙara tashi ba.”
12 E de Benjamin disse: O amado do Senhor habitará seguro com ele: todo o dia o cobrirá, e morará entre os seus ombros.
Game da Benyamin ya ce, “Bari ƙaunataccen Ubangiji yă zauna lafiya kusa da shi, gama yana tsare shi dukan yini, wanda kuma Ubangiji yake ƙauna yana zama a tsakanin kafaɗunsa.”
13 E de José disse: bendita do Senhor seja a sua terra, com o mais excelente dos céus, como orvalho, e com o abismo que jaz abaixo.
Game da Yusuf ya ce, “Bari Ubangiji yă albarkaci ƙasarsa da raɓa mai daraja daga sama a bisa da kuma zurfin ruwan da suke kwance a ƙarƙashi;
14 E com as mais excelentes novidades do sol, e com as mais excelentes produções da lua,
da abubuwa masu kyau da rana take kawo, da kuma abubuwa mafi kyau da wata zai iya haifar;
15 E com o mais excelente dos montes antigos, e com o mais excelente dos outeiros eternos,
da zaɓaɓɓun kyautai na daɗaɗɗun duwatsu, da kyawawan amfani na madawwaman tuddai.
16 E com o mais excelente da terra, e com a sua plenidão, e com a benevolência daquele que habitava na sarça, a benção venha sobre a cabeça de José, e sobre o alto da cabeça do que foi separado de seus irmãos
Tare da kyautai mafi kyau na duniya da cikarta, da tagomashi na wanda yake zama a ƙaramin itace mai ƙonewa. Bari duk waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin sarki a cikin’yan’uwansa.
17 Ele tem a glória do primogênito do seu boi, e as suas pontas são pontas de unicórnio: com eles escorneará os povos juntamente até às extremidades da terra: estes pois são os dez milhares de Ephraim, e estes são os milhares de Manasseh.
Cikin daraja yana yi kamar ɗan fari na bijimi; ƙahoninsa ƙahonin ɓauna ne. Tare da su zai tukwiyi al’ummai, har ma da waɗanda suke ƙarshen duniya. Haka dubu dubban Efraim suke; haka dubban Manasse suke.”
18 E de Zebulon disse: Zebulon, alegra-te nas tuas saídas; e tu, Issacar, nas tuas tendas.
Game da Zebulun ya ce, “Ka yi farin ciki, Zebulun, a fitowarka, kai kuma Issakar, a cikin tentunanka.
19 Eles chamarão os povos ao monte: ali oferecerão ofertas de justiça, porque chuparão a abundância dos mares e os tesouros escondidos da areia.
Za su kira mutane zuwa dutse, a can za su miƙa hadayun adalci; za su yi biki a yalwan tekuna, a dukiyoyin da aka ɓoye a cikin yashi.”
20 E de Gad disse: bendito aquele que faz dilatar a Gad, habita como a leoa, e despedaça o braço e alto da cabeça.
Game da Gad ya ce, “Mai albarka ne wanda ya fadada mazaunin Gad! Gad yana zama a can kamar zaki, yana yayyage a hannu da kai.
21 E se proveu do primeiro, porquanto ali estava escondida a porção do legislador: pelo que veio com os chefes do povo, executou a justiça do Senhor e os seus juízos para com Israel.
Ya zaɓi ƙasa mafi kyau wa kansa; aka ajiye masa rabon shugaba. Sa’ad da shugabannin mutane suka taru, ya aikata adalcin Ubangiji da kuma hukuncinsa game da Isra’ila.”
22 E de Dan disse: Dan é leãozinho; saltará de Basan.
Game da Dan ya ce, “Dan ɗan zaki ne, yana tsalle daga Bashan.”
23 E de Naphtali disse: Farta-te, ó Naphtali, da benevolência, e enchete da benção do Senhor; possui o ocidente e o meio dia.
Game da Naftali ya ce, “Naftali ƙosasshe ne da tagomashin Ubangiji, ya kuma cika albarkarsa; zai gāji gefen kudu zuwa tafki.”
24 E de Aser disse: bendito seja Aser com seus filhos, agrade a seus irmãos, e banhe em azeite o seu pé.
Game da Asher ya ce, “Mafi albarka na’ya’yan, shi ne Asher; bari yă sami tagomashi daga’yan’uwansa, bari kuma yă wanke ƙafafunsa a cikin mai.
25 O ferro e o metal será o teu calçado; e a tua força será como os teus dias.
Madogaran ƙofofinka za su zama ƙarfe da tagulla, ƙarfinka kuma zai zama daidai da kwanakinka.
26 Não há outro, ó Jeshurun, semelhante a Deus! que cavalga sobre os céus para a tua ajuda, e com a sua alteza sobre as mais altas nuvens.
“Babu wani kamar Allah na Yeshurun, wanda yake hawa a bisa sammai don yă taimake ka a kan gizagizai kuma a cikin darajarsa.
27 O Deus eterno te seja por habitação, e por baixo sejam os braços eternos: e ele lance o inimigo de diante de ti, e diga: Destroe-o.
Allah madawwami shi ne mafakarka, a ƙarƙashina kuma madawwamin hannuwa ne. Zai kore abokin gābanka a gabanka, yana cewa, ‘Ka hallaka shi!’
28 Israel pois habitará só seguro, na terra da fonte de Jacob, na terra de grão e de mosto: e os seus céus gotejarão orvalho.
Haka Isra’ila zai zauna lafiya shi kaɗai; zuriyar Yaƙub a tsare a ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi, inda sammai za su zuba raɓa.
29 Bem-aventurado tu, ó Israel! quem é como tu? um povo salvo pelo Senhor, o escudo do teu socorro, e a espada da tua alteza: pelo que os teus inimigos te serão sujeitos, e tu pisarás sobre as suas alturas.
Kai mai albarka ne, ya Isra’ila! Wane ne yake kamar ka, mutanen da Ubangiji ya ceta? Shi ne mafakarka da mai taimakonka da kuma takobinka mai ɗaukaka. Abokan gābanka za su zo neman jinƙai a gabanka, za ka kuwa tattake masujadansu.”

< Deuteronômio 33 >