< 2 Reis 15 >
1 No ano vinte e sete de Jeroboão, rei de Israel, começou a reinar Azarias, filho d'Amasias, rei de Judá.
A shekara ta ashirin da bakwai ta mulkin Yerobowam sarkin Isra’ila, Azariya ɗan Amaziya, sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Tinha dezeseis anos quando começou a reinar, e cincoênta e dois anos reinou em Jerusalém: e era o nome de sua mãe Jecolia, de Jerusalém.
Yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya daga Urushalima.
3 E fez o que era reto aos olhos do Senhor, conforme tudo o que fizera Amasias, seu pai.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
4 Tão somente os altos se não tiraram: porque ainda o povo sacrificava e queimava incenso nos altos.
Amma bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane kuwa suka yi ta yin hadaya da ƙona turare a can.
5 E o Senhor feriu o rei, e ficou leproso até ao dia da sua morte; e habitou numa casa separada: porém Jothão, filho do rei, tinha o cargo da casa, julgando o povo da terra.
Ubangiji ya sa wa sarki ciwon kuturta har mutuwarsa, ya kuma zauna a keɓe. Yotam ɗan sarki, shi ne ya gudanar da sha’anin fada, ya kuma shugabanci mutanen ƙasar.
6 Ora o mais dos sucessos de Azarias, e tudo o que fez, porventura não está escrito no livro das crônicas dos reis de Judá?
Game da sauran ayyukan mulkin Azariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
7 E Azarias dormiu com seus pais, e o sepultaram junto a seus pais, na cidade de David: e Jothão, seu filho, reinou em seu lugar.
Azariya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi kusa da su a Birnin Dawuda. Yotam ɗansa, kuma ya gāje shi.
8 No ano trinta e oito d'Azarias, rei de Judá, reinou Zacarias, filho de Jeroboão, sobre Israel, em Samaria, seis meses.
A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Zakariya ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki wata shida.
9 E fez o que parecia mal aos olhos do Senhor, como tinham feito seus pais; nunca se apartou dos pecados de Jeroboão, filho de Nebat, que fez pecar a Israel.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi. Bai bar aikata zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi ba.
10 E Sallum, filho de Jabés, conspirou contra ele e o feriu diante do povo, e o matou; e reinou em seu lugar.
Sai Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla wa Zakariya maƙarƙashiya. Ya tasam masa a gaban jama’a, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
11 Ora o mais dos sucessos de Zacarias, eis que está escrito no livro das crônicas dos reis de Israel.
Game da sauran ayyukan mulkin Zakariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
12 Esta foi a palavra do Senhor, que falou a Jehu, dizendo: Teus filhos, até à quarta geração, se assentarão sobre o trono de Israel. E assim foi.
Ta haka maganar Ubangiji da ya yi wa Yehu ta cika, wadda ya ce, “Zuriyarka za tă zauna a kursiyin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
13 Sallum, filho de Jabés, começou a reinar no ano trinta e nove de Uzias, rei de Judá: e reinou um mês inteiro em Samaria.
Shallum ɗan Yabesh ya zama sarki a shekara ta talatin da tara ta mulkin Uzziya sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki na wata ɗaya a Samariya.
14 Porque Menahem, filho de Gadi, subiu de Tirza, e veio a Samaria; e feriu a Sallum, filho de Jabés, em Samaria, e o matou, e reinou em seu lugar.
Sa’an nan Menahem ɗan Gadi ya gangara daga Tirza ya haura zuwa Samariya. Ya tasam wa Shallum ɗan Yabesh a Samariya, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
15 Ora o mais dos sucessos de Sallum, e a conspiração que fez, eis que está escrito no livro das crônicas dos reis de Israel.
Game da sauran ayyukan mulkin Shallum, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
16 Então Menahem feriu a Tiphsah, e a todos os que nela havia, como também a seus termos desde Tirza, porque não lhe tinham aberto; e os feriu pois, e a todas as mulheres grávidas fendeu pelo meio.
A lokacin nan sai Menahem ya taso daga Tirza, ya kai wa Tifsa hari da kowa wanda yake a birnin da kewayenta, don sun ƙi su buɗe ƙofofinsu. Ya kori Tifsa daga aiki, ya kuma tsattsaga cikin dukan mata masu juna biyu.
17 Desde o ano trinta e nove de Azarias, rei de Judá, Menahem, filho de Gadi, começou a reinar sobre Israel, e reinou dez anos em Samaria.
A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Menahem ɗan Gadi ya zama sarkin Isra’ila, ya yi mulki a Samariya shekara goma.
18 E fez o que parecia mal aos olhos do Senhor: todos os seus dias se não apartou dos pecados de Jeroboão, filho de Nebat, que fez pecar a Israel.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. A duk tsawon mulkinsa, bai rabu da zunuban da Yerobowam ɗan Nebat ya sa Isra’ila suka aikata ba.
19 Então veio Pul, rei d'Assyria, contra a terra: e Menahem deu a Pul mil talentos de prata, para que a sua mão fosse com ele, a fim de firmar o reino na sua mão.
Sai Ful sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar hari, Menahem kuwa ya ba shi talenti dubu na azurfa don yă sami goyon bayansa, yă kuma ƙarfafa kahuwa mulkin.
20 E Menahem tirou este dinheiro de Israel, de todos os poderosos e ricos, para o dar ao rei da Assyria, por cada homem cincoênta siclos de prata: assim voltou o rei d'Assyria, e não ficou ali na terra.
Menahem ya tara kuɗin ne ta hanyar haraji a Isra’ila inda ya sa kowane attajiri ya ba da shekel hamsin don a ba sarkin Assuriya. Sa’an nan sarkin Assuriya ya janye, bai ƙara kasance a ƙasar ba.
21 Ora o mais dos sucessos de Menahem, e tudo quanto fez, porventura não está escrito no livro das crônicas dos reis de Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Menahem, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
22 E Menahem dormiu com seus pais: e Pekaia, seu filho, reinou em seu lugar.
Menahem ya huta tare da kakanninsa. Fekahiya ɗansa kuma ya gāje shi.
23 No ano cincoênta de Azarias, rei de Judá, começou a reinar Pekaia, filho de Menahem, e reinou sobre Israel, em Samaria, dois anos.
A shekara ta hamsin ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Fekahiya ɗan Menahem ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekara biyu.
24 E fez o que parecia mal aos olhos do Senhor: nunca se apartou dos pecados de Jeroboão, filho de Nebat, que fez pecar a Israel.
Fekahiya ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat wanda ya sa Isra’ila ya aikata ba.
25 E Peka, filho de Remalias, seu capitão, conspirou contra ele, e o feriu em Samaria, no paço da casa do rei, juntamente com Argob e com Arieh, e com ele cincoênta homens dos filhos dos gileaditas: e o matou, e reinou em seu lugar.
Ɗaya daga cikin manyan fadawansa, Feka ɗan Remaliya, ya ƙulla masa maƙarƙashiya. Ɗauke da mutanen Gileyad hamsin, ya kashe Fekahiya tare da Argob da kuma Ariye a fadan sarki a Samariya. Ta haka Feka ya kashe Fekahiya ya kuma gāje shi.
26 Ora o mais dos sucessos de Pekaia, e tudo quanto fez, eis que está escrito no livro das crônicas dos reis de Israel.
Game da sauran ayyukan mulkin Fekahiya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
27 No ano cincoênta e dois de Azarias, rei de Judá, começou a reinar Peka, filho de Remalias, e reinou sobre Israel, em Samaria, vinte anos.
A shekara ta hamsin da biyu ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Feka ɗan Remaliya ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya yi mulki shekara ashirin.
28 E fez o que parecia mal aos olhos do Senhor: nunca se apartou dos pecados de Jeroboão, filho de Nebat, que fez pecar a Israel.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai kauce wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta yi ba.
29 Nos dias de Peka, rei de Israel, veio Tiglath-pileser, rei d'Assyria, e tomou a Ijon, e a Abel-beth-maaca, e a Janoah, e a Kedes, e a Hasor, e a Gilead, e a Galiléia, e a toda a terra de Naphtali, e os levou a Assyria.
A zamanin Feka sarkin Isra’ila, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo ya kama Iyon, Abel-Bet-Ma’aka, Yanowa da Kedesh da kuma Hazor. Ya kame Gileyad da Galili, haɗe da dukan ƙasar Naftali, ya kuma kwashi mutanen zuwa Assuriya.
30 E Hoseas, filho de Ela, conspirou contra Peka, filho de Remalias, e o feriu, e o matou, e reinou em seu lugar, no vigésimo ano de Jothão, filho de Uzias.
Sa’an nan Hosheya ɗan Ela ya ƙulla wa Feka ɗan Remaliya maƙarƙashiya. Ya fāɗa masa ya kuma kashe shi, sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki a shekara ta shirin ta mulkin Yotam ɗan Uzziya.
31 Ora o mais dos sucessos de Peka, e tudo quanto fez, eis que está escrito no livro das crônicas dos reis de Israel.
Game da sauran ayyukan mulkin Feka da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
32 No ano segundo de Peka, filho de Remalias, rei de Israel, começou a reinar Jothão, filho de Uzias, rei de Judá.
A shekara ta biyu ta mulkin Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila, Yotam ɗan Uzziya sarkin Yahuda ya fara mulki.
33 Tinha vinte e cinco anos de idade quando começou a reinar, e reinou dezeseis anos em Jerusalém: e era o nome de sua mãe Jerusa, filha de Zadok.
Ya zama sarki yana da shekara ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Sunan mahaifiyarsa Yerusha,’yar Zadok.
34 E fez o que era reto aos olhos do Senhor: fez conforme tudo quanto fizera seu pai Uzias.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa Uzziya ya yi.
35 Tão somente os altos se não tiraram; porque ainda o povo sacrificava e queimava incenso nos altos: este edificou a porta alta da casa do Senhor.
Duk da haka, bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙona turare a can. Yotam ya sāke gina Ƙofar Bisa ta haikalin Ubangiji.
36 Ora o mais dos sucessos de Jothão, e tudo quanto fez, porventura não está escrito no livro das crônicas dos reis de Judá?
Game da sauran ayyukan mulkin Yotam da aikin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
37 Naqueles dias começou o Senhor a enviar contra Judá, a Resin, rei da Síria, e a Peka, filho de Remalias.
(A kwanakin nan Ubangiji ya fara aikan Rezin sarkin Aram da Feka ɗan Remaliya, su yi gāba da Yahuda.)
38 E Jothão dormiu com seus pais, e foi sepultado junto a seus pais, na cidade de David, seu pai: e Achaz, seu filho, reinou em seu lugar.
Yotam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda, birnin mahaifinsa. Ahaz ɗansa kuma ya gāje shi.