< Zacarias 13 >

1 N'aquelle dia haverá uma fonte aberta para a casa de David, e para os habitantes de Jerusalem, contra o peccado, e contra a immundicia.
“A ranan nan za a buɗe maɓulɓulan ruwa zuwa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima, don a tsarkake su daga zunubi da rashin tsabta.
2 E será n'aquelle dia, diz o Senhor dos Exercitos, que desfarei da terra os nomes dos idolos, e d'elles não se fará mais memoria; e tambem farei sair da terra os prophetas e o espirito da immundicia.
“A ranan nan, zan kawar da sunayen gumaka daga ƙasar, ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kawar da annabawa da kuma ruhu marar tsabta daga ƙasar.
3 E será que, quando alguem prophetizar mais, seu pae e sua mãe, que o geraram, lhe dirão: Não viverás, porque fallaste mentira em nome do Senhor; e seu pae e sua mãe, que o geraram, o traspassarão quando prophetizar.
In kuma wani ya yi annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa’ad da yake yin annabci, iyayensa za su soke shi da takobi.
4 E será n'aquelle dia que os prophetas se envergonharão, cada um da sua visão, quando prophetizar; nem elles se vestirão mais de manto de pellos, para mentirem.
“A ranan nan kowane annabi zai ji kunyar annabcin wahayinsa. Ba zai sa rigar annabci mai gashi ba don yă yi ruɗu.
5 E dirão: Não sou propheta, lavrador sou da terra; porque certo homem para isso me adquiriu desde a minha mocidade.
Zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne. Ni manomi ne; ƙasa ce nake samun abin zaman gari tun ina matashi.’
6 E se alguem lhe disser: Que são estas feridas nas tuas mãos? Dirá elle: Feridas são com que fui ferido em casa dos meus amadores.
In wani ya tambaye shi, ‘Waɗanne miyaku ne haka a jikinka?’ Zai amsa yă ce, ‘Miyakun da aka yi mini a gidan abokaina ne.’
7 Ó espada, desperta-te contra o meu Pastor e contra o varão que é o meu companheiro, diz o Senhor dos Exercitos: fere ao Pastor, e espalhar-se-hão as ovelhas; mas volverei a minha mão para os pequenos.
“Tashi, ya takobi, gāba da makiyayina, mutumin da yake kusa da ni sosai!” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Kashe makiyayin, sai tumakin su watse, in kuma tayar wa ƙananan.
8 E será em toda a terra, diz o Senhor, que as duas partes d'ella serão extirpadas, e expirarão; mas a terceira parte restará n'ella.
A cikin ƙasar duka,” in ji Ubangiji, “kashi biyu bisa uku za a buge su su hallaka; duk da haka za a bar kashi ɗaya bisa uku a cikinta.
9 E farei passar esta terceira parte pelo fogo, e a purificarei, como se purifica a prata, e a provarei, como se prova o oiro: ella invocará o meu nome, e eu a ouvirei; direi: Meu povo é, e ella dirá: O Senhor é o meu Deus.
Wannan kashi ɗaya bisa ukun zan kawo in sa a cikin wuta; zan tace su kamar azurfa in gwada su kamar zinariya. Za su kira bisa sunana zan kuwa amsa musu; zan ce, ‘Su mutanena ne,’ za su kuma ce, ‘Ubangiji ne Allahnmu.’”

< Zacarias 13 >