< Rute 4 >

1 E Boaz subiu á porta, e assentou-se ali: e eis que o remidor de que Boaz tinha fallado ia passando, e disse-lhe: Ó fulano, desvia-te para cá, assenta-te aqui. E desviou-se para ali, e assentou-se.
Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
2 Então tomou dez homens dos anciãos da cidade, e disse: Assentae-vos aqui. E assentaram-se.
Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
3 Então disse ao remidor: Aquella parte da terra que foi de Elimelech, nosso irmão, Noemi, que tornou da terra dos moabitas, a vendeu.
Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
4 E disse eu: Manifestal-o-hei em teus ouvidos, dizendo: Toma-a diante dos habitantes, e diante dos anciãos do meu povo; se a has de redimir, redime-a, e, se não se houver de redimir, declara-m'o, para que o saiba, pois outro não ha senão tu que a redima, e eu depois de ti. Então disse elle: Eu a redimirei.
Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
5 Disse porém Boaz: No dia em que tomares a terra da mão de Noemi, tambem a tomarás da mão de Ruth, a moabita, mulher do defunto, para suscitar o nome do defunto sobre a sua herdade.
Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
6 Então disse o remidor: Para mim não a poderei redimir, para que não damne a minha herdade: redime tu a minha remissão para ti, porque eu não a poderei redimir.
Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
7 Havia, pois, já de muito tempo este costume em Israel, emquanto a remissão e contracto, para confirmar todo o negocio, que o homem descalçava o sapato e o dava ao seu proximo: e isto era por testemunho em Israel.
(To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
8 Disse pois o remidor a Boaz: Toma-a para ti. E descalçou o sapato.
Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
9 Então Boaz disse aos anciãos e a todo o povo: Sois hoje testemunhas de que tomei tudo quanto foi d'Elimelech, e de Chilion, e de Mahlon, da mão de Noemi,
Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
10 E de que tambem tomo por mulher a Ruth, a moabita, que foi mulher de Mahlon, para suscitar o nome do defunto sobre a sua herdade, para que o nome do defunto não seja desarraigado d'entre seus irmãos e da porta do seu logar: d'isto sois hoje testemunhas.
Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
11 E todo o povo que estava na porta, e os anciãos, disseram: Somos testemunhas: o Senhor faça a esta mulher, que entra na tua casa, como a Rachel e como a Leah, que ambas edificaram a casa d'Israel; e ha-te já valorosamente em Ephrata, e faze-te nome afamado em Beth-lehem.
Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
12 E seja a tua casa como a casa de Perez (que Tamar pariu a Judah), da semente que o Senhor te der d'esta moça.
Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
13 Assim tomou Boaz a Ruth, e ella lhe foi por mulher; e elle entrou a ella, e o Senhor lhe deu conceição, e pariu um filho.
Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
14 Então as mulheres disseram a Noemi: Bemdito seja o Senhor, que não deixou hoje de te dar remidor, e seja o seu nome afamado em Israel.
Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
15 Elle te será por recreador da alma, e conservará a tua velhice, pois tua nora, que te ama, o pariu, e ella te é melhor do que sete filhos.
Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
16 E Noemi tomou o filho, e o poz no seu regaço, e foi sua ama.
Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
17 E as visinhas lhe deram um nome, dizendo: A Noemi nasceu um filho. E chamaram o seu nome Obed. Este é o pae de Jessé, pae de David.
Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
18 Estas são pois as gerações de Perez: Perez gerou a Esrom,
Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
19 E Esrom gerou a Arão, e Arão gerou a Amminadab,
Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
20 E Amminadab gerou a Nahasson, e Nahasson gerou a Salmon,
Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
21 E Salmon gerou a Boaz, e Boaz gerou a Obed,
Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
22 E Obed gerou a Jessé, e Jessé gerou a David.
Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.

< Rute 4 >