< Romanos 11 >
1 Digo pois: Porventura rejeitou Deus o seu povo? De modo nenhum; porque tambem eu sou israelita, da descendencia d'Abrahão, da tribu de Benjamin.
To, ina da tambaya. Allah ya ƙi mutanensa ne? Sam, ko kaɗan! Ni mutumin Isra’ila ne kaina, zuriyar Ibrahim kuwa, daga kabilar Benyamin.
2 Deus não rejeitou o seu povo, o qual antes conheceu. Ou não sabeis o que a Escriptura diz de Elias? Como falla a Deus contra Israel, dizendo:
Allah bai ƙi mutanensa da ya rigya sani ba. Ba ku san abin da Nassi ya faɗa game da Iliya ba, yadda ya kawo kuka ga Allah a kan Isra’ila ya ce,
3 Senhor, mataram os teus prophetas, e derribaram os teus altares; e só eu fiquei, e buscam a minha alma.
“Ya Ubangiji, sun karkashe annabawanka suka kuma rurrushe bagadanka; ni kaɗai na ragu, suna kuma neman raina”?
4 Mas que lhe diz a resposta divina? Reservei para mim sete mil varões, que não dobraram os joelhos diante de Baal.
Wace amsa ce Allah ya ba shi? “Na keɓe wa kaina dubu bakwai waɗanda ba su yi wa Ba’al sujada ba.”
5 Assim pois tambem agora n'este tempo ficou um resto, segundo a eleição da graça.
Haka ma, a wannan zamani akwai ragowar da aka zaɓa ta wurin alheri.
6 E, se é por graça, já não é pelas obras: de outra maneira, a graça já não é graça. E, se é pelas obras, já não é graça: de outra maneira a obra já não é obra.
In kuwa na alheri ne, ba sauran cewa ya dogara ga ayyuka ke nan. In ba haka ba, ashe, alheri ba alheri ba ne kuma.
7 Pois que? O que Israel buscava não o alcançou; mas os eleitos o alcançaram, e os outros foram endurecidos.
To, sai me? Abin da Isra’ila suka nema da himma ba su samu ba, amma zaɓaɓɓun suka samu. Sauran suka taurare,
8 Como está escripto: Deus lhes deu espirito de profundo somno; olhos para não vêrem, e ouvidos para não ouvirem, até ao dia d'hoje.
kamar yadda yake a rubuce cewa, “Allah ya ba su ruhun ruɗewa, idanu don su kāsa gani, da kuma kunnuwa don su kāsa ji, har yă zuwa yau.”
9 E David diz: Torne-se-lhes a sua mesa em laço, e em armadilha, e em tropeço e em sua retribuição;
Dawuda kuma ya ce, “Bari teburin cin abincinsu yă zama musu tarko, sanadin fāɗuwa da dutsen sa tuntuɓe da kuma ramuwa a kansu.
10 Escureçam-se-lhes os olhos para não verem, e encurvem-se-lhes continuamente as costas.
Bari idanunsu su duhunta don kada su iya gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.”
11 Digo pois: Porventura tropeçaram, para que caissem? De modo nenhum, mas pela sua queda veiu a salvação aos gentios, para os incitar á emulação.
Har yanzu ina da tambaya. Sun yi tuntuɓe har ya kai ga fāɗuwar da ba za su iya tashi ba ne? Sam, ko kaɗan! A maimako, saboda laifinsu ne ceto ya zo ga Al’ummai don a sa mutanen Isra’ila su ji kishi.
12 E, se a sua queda é a riqueza do mundo, e a sua diminuição a riqueza dos gentios, quanto mais a sua plenitude?
Amma in laifinsu yana nufin albarka ga duniya, hasararsu kuma albarka ga Al’ummai, ina misalin yalwar da albarkunsu za su kawo!
13 Porque comvosco fallo, gentios, que, emquanto fôr apostolo dos gentios, glorificarei o meu ministerio;
Ina magana da ku ne fa Al’ummai. Tun da yake ni manzo ne ga Al’ummai, ina taƙama da aikin nan nawa,
14 Para vêr se de alguma maneira posso incitar á emulação os da minha carne, e salvar alguns d'elles.
da fata zan rura kabilata a ta kowace hanya su ji kishi har ma yă sa in ceci waɗansunsu.
15 Porque, se a sua rejeição é a reconciliação do mundo, qual será a sua admissão, senão a vida d'entre os mortos?
Gama in ƙinsu da aka yi ya zama sulhu ga duniya, me karɓarsu za tă zama in ba rai daga matattu ba?
16 E, se as primicias são sanctas, tambem a massa o é; se a raiz é sancta, tambem os ramos o são.
In sashen da aka miƙa a matsayin nunan fari tsattsarka ne, to, sauran ma tsattsarka ne; in saiwar tsattsarka ce, to, sauran rassan ma tsattsarka ne.
17 E, se alguns dos ramos foram quebrados, e tu, sendo zambujeiro, foste enxertado em logar d'elles, e feito participante da raiz e da seiva da oliveira,
In an sassare waɗansu rassa, kai kuwa da kake kai zaitun jeji, aka ɗauke ka aka kuma yi muku aure, a yanzu kuwa kana shan ni’imar saiwar zaitun ɗin nan tare da sauran rassan,
18 Não te glories contra os ramos; e, se contra elles te gloriares, não és tu que sustentas a raiz, mas a raiz a ti
kada ka yi taƙama cewa ka fi waɗancan rassan da aka sassare. In kuwa ka yi haka, to, ka yi la’akari da wannan. Ba kai ne kake taimakon saiwar ba, saiwar ce take taimakonka.
19 Dirás pois: Os ramos foram quebrados, para que eu fosse enxertado.
To, kana iya cewa, “An sassare rassan ne don a ɗaura aure da ni.”
20 Bem: por incredulidade foram quebrados, e tu estás em pé pela fé: não te ensoberbeças, mas teme
Haka yake. Amma an sassare su ne saboda rashin bangaskiya, kai kuma kana tsaye ta wurin bangaskiya. Kada ka yi taƙama, sai dai ka ji tsoro.
21 Porque, se Deus não poupou os ramos naturaes, teme que te não poupe a ti tambem.
Gama in har Allah bai bar rassan nan na asali ba, kai ma ba zai bar ka ba.
22 Considera pois a bondade e a severidade de Deus: para com os que cairam, severidade; porém para comtigo, a benignidade de Deus, se permaneceres na sua benignidade; de outra maneira, tambem tu serás cortado.
Ka lura fa da alheri da kuma tsananin Allah, tsanani ga waɗanda suka fāɗi, amma alheri a gare ka, da fata za ka ci gaba cikin alherinsa. In ba haka ba, kai ma za a sare ka.
23 Porém tambem elles, se não permanecerem na incredulidade, serão enxertados; porque poderoso é Deus para os tornar a enxertar.
In kuwa ba su nace cikin rashin bangaskiya ba, za a sāke ɗaura aure da su, domin Allah yana iya sāke haɗa su.
24 Porque, se tu foste cortado do natural zambujeiro, e, contra a natureza, enxertado na boa oliveira, quanto mais esses, que são naturaes, serão enxertados na sua propria oliveira?
Kai ma da aka saro daga zaitun ɗin da asalinsa yake na jeji, aka ɗaura aure da kai a jikin zaitun ɗin na gida, saɓanin yadda aka saba, balle waɗannan rassa na asali, da za a ɗaura aure da su a jikin zaitun ɗin nan nasu na asali?
25 Porque não quero, irmãos, que ignoreis este segredo (para que não presumaes de vós mesmos): que o endurecimento veiu em parte sobre Israel, até que a plenitude dos gentios haja entrado.
Ba na so ku kasance cikin rashin sani game da wannan asirin’yan’uwa, domin kada ku ɗaga kai. Isra’ila sun ɗanɗana sashe na taurarewa har sai da shigowar Al’ummai masu yawa ya cika.
26 E assim todo o Israel será salvo, como está escripto: De Sião virá o Libertador, e desviará de Jacob as impiedades.
Ta haka kuwa za a ceci dukan Isra’ila, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai ceto zai zo daga Sihiyona; zai kawar da rashin bin Allah daga Yaƙub.
27 E este será o meu concerto com elles, quando eu tirar os seus peccados.
Wannan kuwa shi ne alkawarina da su sa’ad da na ɗauke musu zunubansu.”
28 Assim que, quanto ao evangelho, são inimigos por causa de vós; mas, quanto á eleição, amados por causa dos paes
Game da zancen nan na bishara kuwa, su abokan gāba ne saboda ku; amma game da zaɓen kuwa, su ƙaunatattunsa ne, albarkacin kakannin kakanninsu,
29 Porque os dons e a vocação de Deus são sem arrependimento.
gama kyautar Allah da kiransa ba a sokewa.
30 Porque assim como vós tambem antigamente fostes desobedientes a Deus, porém agora alcançastes misericordia pela desobediencia d'elles,
Kamar yadda a dā can ku da kuke marasa biyayya ga Allah kuka sami jinƙai yanzu ta dalilin rashin biyayyarsu,
31 Assim tambem estes agora foram desobedientes, para tambem alcançarem misericordia pela vossa misericordia.
haka su ma suka zama marasa biyayya a yanzu domin su ma su sami jinƙai ta dalilin jinƙan da Allah ya yi muku.
32 Porque Deus encerrou a todos debaixo da desobediencia, para com todos usar de misericordia. (eleēsē )
Gama Allah ya daure dukan mutane ga rashin biyayya don yă nuna jinƙai ga kowa. (eleēsē )
33 Ó profundidade das riquezas, tanto da sabedoria, como da sciencia de Deus! Quão insondaveis são os seus juizos, e quão inexcrutaveis os seus caminhos!
Kai, zurfin yalwar hikima da kuma sanin Allah yana nan a yalwace! Hukunce-hukuncensa kuma su fi gaban bincike, hanyoyinsa kuwa sun wuce gaban ganewa!
34 Porque quem comprehendeu o intento do Senhor? ou quem foi seu conselheiro?
“Wa ya taɓa sanin zuciyar Ubangiji? Ko kuwa yă ba shi shawara?”
35 Ou quem lhe deu primeiro a elle, e lhe será recompensado?
“Wa ya taɓa ba wa Allah wani abu, da Allah zai sāka masa?”
36 Porque d'elle e por elle, e para elle, são todas as coisas; gloria pois a elle eternamente. Amen. (aiōn )
Gama daga gare shi, ta wurinsa, da kuma saboda shi ne dukan abubuwa suka kasance. Ɗaukaka ta tabbata a gare shi har abada! Amin. (aiōn )