< Salmos 9 >

1 Eu te louvarei, Senhor, com todo o meu coração; contarei todas as tuas maravilhas.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
2 Em ti me alegrarei e saltarei de prazer; cantarei louvores ao teu nome, ó Altissimo.
Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
3 Porquanto os meus inimigos voltaram para traz, cairam e pereceram diante da tua face.
Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
4 Pois tu tens sustentado o meu direito e a minha causa; tu te assentaste no tribunal, julgando justamente.
Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
5 Reprehendeste as nações, destruiste os impios; apagaste o seu nome para sempre e eternamente.
Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
6 Oh! inimigo! acabaram-se para sempre as assolações; --e tu arrazaste as cidades, e a sua memoria pereceu com ellas.
Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
7 Mas o Senhor está assentado perpetuamente; já preparou o seu tribunal para julgar.
Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
8 Elle mesmo julgará o mundo com justiça; fará juizo aos povos com rectidão.
Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
9 O Senhor será tambem um alto refugio para o opprimido; um alto refugio em tempos de angustia.
Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
10 E em ti confiarão os que conhecem o teu nome; porque tu, Senhor, nunca desamparaste aos que te buscam.
Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
11 Cantae louvores ao Senhor, que habita em Sião; annunciae entre os povos os seus feitos.
Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
12 Pois quando busca derramamento de sangue, lembra-se d'elles; não se esquece do clamor dos miseraveis.
Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
13 Tem misericordia de mim, Senhor, olha para a minha miseria, que soffro d'aquelles que me aborrecem; tu que me levantas das portas da morte,
Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
14 Para que eu conte todos os teus louvores nas portas da filha de Sião, e me alegre na tua salvação.
don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
15 As gentes enterraram-se na cova que fizeram; na rede que ocultaram ficou preso o seu pé.
Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
16 O Senhor é conhecido pelo juizo que fez; enlaçado foi o impio nas obras de suas mãos (Higgaion, Selah)
An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
17 Os impios serão lançados no inferno, e todas as gentes que se esquecem de Deus. (Sheol h7585)
Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
18 Porque o necessitado não será esquecido para sempre, nem a expectação dos miseraveis perecerá perpetuamente.
Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
19 Levanta-te, Senhor; não prevaleça o homem; sejam julgadas as gentes diante da tua face.
Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
20 Põe-os em medo, Senhor, para que saibam as nações que não são mais do que homens (Selah)
Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)

< Salmos 9 >