< Salmos 78 >

1 Escutae a minha lei, povo meu: inclinae os vossos ouvidos ás palavras da minha bocca.
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 Abrirei a minha bocca n'uma parabola; fallarei enigmas da antiguidade.
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 As quaes temos ouvido e sabido, e nossos paes nol-as teem contado.
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 Não as encobriremos aos seus filhos, mostrando á geração futura os louvores do Senhor, assim como a sua força e as maravilhas que fez.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Porque elle estabeleceu um testemunho em Jacob, e poz uma lei em Israel, a qual deu aos nossos paes para que a fizessem conhecer a seus filhos.
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 Para que a geração vindoura a soubesse, os filhos que nascessem, os quaes se levantassem e a contassem a seus filhos.
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 Para que pozessem em Deus a sua esperança, e se não esquecessem das obras de Deus, mas guardassem os seus mandamentos.
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 E não fossem como seus paes, geração contumaz e rebelde, geração que não regeu o seu coração, e cujo espirito não foi fiel com Deus
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 Os filhos de Ephraim, armados e trazendo arcos, viraram costas no dia da peleja.
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 Não guardaram o concerto de Deus, e recusaram andar na sua lei.
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 E esqueceram-se das suas obras e das maravilhas que lhes fizera ver.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 Maravilhas que elle fez á vista de seus paes na terra do Egypto, no campo de Zoan.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Dividiu o mar, e os fez passar por elle; fez com que as aguas parassem como n'um montão.
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 De dia os guiou por uma nuvem, e toda a noite por uma luz de fogo.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 Fendeu as penhas no deserto; e deu-lhes de beber como de grandes abysmos.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 Fez sair fontes da rocha, e fez correr as aguas como rios.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 E ainda proseguiram em peccar contra elle, provocando ao Altissimo na solidão.
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 E tentaram a Deus nos seus corações, pedindo carne para o seu appetite.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 E fallaram contra Deus, e disseram: Acaso pode Deus preparar-nos uma mesa no deserto?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Eis que feriu a penha, e aguas correram d'ella; rebentaram ribeiros em abundancia: poderá tambem dar-nos pão, ou preparar carne para o seu povo?
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 Pelo que o Senhor os ouviu, e se indignou: e accendeu um fogo contra Jacob, e furor tambem subiu contra Israel;
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 Porquanto não creram em Deus, nem confiaram na sua salvação:
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Ainda que mandara ás altas nuvens, e abriu as portas dos céus,
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 E chovera sobre elles o manná para comerem, e lhes dera do trigo do céu.
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 O homem comeu o pão dos anjos; elle lhes mandou comida a fartar.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Fez ventar o vento do oriente nos céus, e o trouxe do sul com a sua força.
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 E choveu sobre elles carne como pó, e aves d'azas como a areia do mar.
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 E as fez cair no meio do seu arraial, ao redor de suas habitações.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 Então comeram e se fartaram bem; pois lhes cumpriu o seu desejo.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 Não refreiaram o seu appetite. Ainda lhes estava a comida na bocca,
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 Quando a ira de Deus desceu sobre elles, e matou os mais gordos d'elles, e feriu os escolhidos d'Israel.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 Com tudo isto ainda peccaram, e não deram credito ás suas maravilhas.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 Pelo que consumiu os seus dias na vaidade e os seus annos na angustia.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Quando os matava, então o procuravam; e voltavam, e de madrugada buscavam a Deus.
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 E se lembravam de que Deus era a sua rocha, e o Deus Altissimo o seu Redemptor.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Todavia lisongeavam-n'o com a bocca, e com a lingua lhe mentiam.
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 Porque o seu coração não era recto para com elle, nem foram fieis no seu concerto.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Porém elle, que é misericordioso, perdoou a sua iniquidade: e não os destruiu, antes muitas vezes desviou d'elles o seu furor, e não despertou toda a sua ira
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 Porque se lembrou de que eram de carne, vento que vae e não torna.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Quantas vezes o provocaram no deserto, e o molestaram na solidão!
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 Voltaram atraz, e tentaram a Deus; e limitaram o Sancto d'Israel.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 Não se lembraram da sua mão, nem do dia em que os livrou do adversario:
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 Como obrou os seus signaes no Egypto, e as suas maravilhas no campo de Zoan;
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 E converteu os seus rios em sangue, e as suas correntes, para que não podessem beber.
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 Enviou entre elles enxames de moscas que os consumiram, e rãs que os destruiram.
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 Deu tambem ao pulgão a sua novidade, e o seu trabalho aos gafanhotos.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 Destruiu as suas vinhas com saraiva, e os seus sycomoros com pedrisco.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 Tambem entregou o seu gado á saraiva, e os seus rebanhos ás brazas ardentes.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 Lançou sobre elles o ardor da sua ira, furor, indignação, e angustia, mandando maus anjos contra elles.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 Preparou caminho á sua ira; não retirou as suas almas da morte, mas entregou á pestilencia as suas vidas.
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 E feriu a todo o primogenito no Egypto, primicias da sua força nas tendas de Cão.
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 Mas fez com que o seu povo saisse como ovelhas, e os guiou pelo deserto como um rebanho.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 E os guiou com segurança, que não temeram; mas o mar cobriu os seus inimigos.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 E o trouxe até ao termo do seu sanctuario, até este monte que a sua dextra adquiriu.
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 E expulsou as nações de diante d'elles, e as partiu em herança por linha, e fez habitar em suas tendas as tribus d'Israel.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Comtudo tentaram e provocaram o Deus altissimo, e não guardaram os seus testemunhos.
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 Mas retiraram-se para traz, e portaram-se infielmente como seus paes: viraram-se como um arco enganoso.
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 Pois o provocaram á ira com os seus altos, e moveram o seu zelo com as suas imagens de esculptura.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 Deus ouviu isto e se indignou; e aborreceu a Israel em grande maneira.
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 Pelo que desamparou o tabernaculo em Silo, a tenda que estabeleceu entre os homens.
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 E deu a sua força ao captiveiro; e a sua gloria á mão do inimigo.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 E entregou o seu povo á espada; e se enfureceu contra a sua herança.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 O fogo consumiu os seus mancebos, e as suas donzellas não foram dadas em casamento.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 Os seus sacerdotes cairam á espada, e as suas viuvas não fizeram lamentação.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Então o Senhor despertou, como quem acaba de dormir, como um valente que se alegra com o vinho.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 E feriu os seus adversarios por detraz, e pôl-os em perpetuo desprezo.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Além d'isto, recusou o tabernaculo de José, e não elegeu a tribu d'Ephraim.
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 Antes elegeu a tribu de Judah; o monte de Sião, que elle amava.
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 E edificou o seu sanctuario como altos palacios, como a terra que fundou para sempre.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 Tambem elegeu a David seu servo, e o tirou dos apriscos das ovelhas:
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 E o tirou do cuidado das que se achavam prenhes; para apascentar a Jacob, seu povo, e a Israel, sua herança.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Assim os apascentou, segundo a integridade do seu coração, e os guiou pela industria de suas mãos.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.

< Salmos 78 >