< Salmos 22 >
1 Meu Deus, meu Deus, porque me desamparaste? porque te alongas do meu auxilio e das palavras do meu bramido?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 Meu Deus, eu clamo de dia, e tu não me ouves; de noite, e não tenho socego.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 Porém tu és Sancto, o que habitas entre os louvores d'Israel.
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 Em ti confiaram nossos paes; confiaram, e tu os livraste.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 A ti clamaram e escaparam; em ti confiaram, e não foram confundidos.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 Mas eu sou verme, e não homem, opprobrio dos homens e desprezado do povo.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 Todos os que vêem zombam de mim, arreganham os beiços e meneiam a cabeça, dizendo:
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 Confiou no Senhor, que o livre; livre-o, pois n'elle tem prazer.
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 Mas tu és o que me tiraste do ventre: fizeste-me esperar, estando aos peitos de minha mãe.
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 Sobre ti fui lançado desde a madre; tu és o meu Deus desde o ventre de minha mãe.
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 Não te alongues de mim, pois a angustia está perto, e não ha quem ajude.
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 Muitos toiros me cercaram; fortes toiros de Bazan me rodearam.
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 Abriram contra mim suas boccas, como um leão que despedaça e que ruge.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 Como agua me derramei, e todos os meus ossos se desconjuntaram: o meu coração é como cera, derreteu-se no meio das minhas entranhas.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 A minha força se seccou como um caco, e a lingua se me pega ao paladar: e me pozeste no pó da morte.
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 Pois me rodearam cães: o ajuntamento de malfeitores me cercou, traspassaram-me as mãos e os pés.
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 Poderia contar todos os meus ossos: elles o vêem e me contemplam.
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 Repartem entre si os meus vestidos, e lançam sortes sobre a minha tunica.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 Mas tu, Senhor, não te alongues de mim: força minha, apressa-te em soccorrer-me.
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 Livra-me a minha alma da espada, e a minha predilecta da força do cão.
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 Salva-me da bocca do leão, sim, ouviste-me, desde as pontas dos unicornios.
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 Então declararei o teu nome aos meus irmãos: louvar-te-hei no meio da congregação.
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 Vós, que temeis ao Senhor, louvae-o; todos vós, semente de Jacob, glorificae-o; e temei-o todos vós, semente d'Israel.
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 Porque não desprezou nem abominou a afflicção do afflicto, nem escondeu d'elle o seu rosto; antes, quando elle clamou, o ouviu.
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 O meu louvor virá de ti na grande congregação: pagarei os meus votos perante os que o temem.
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 Os mansos comerão e se fartarão; louvarão ao Senhor os que o buscam: o vosso coração viverá eternamente.
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 Todos os limites da terra se lembrarão, e se converterão ao Senhor: e todas as gerações das nações adorarão perante a tua face.
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 Porque o reino é do Senhor, e elle domina entre as nações.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 Todos os que na terra são gordos comerão e adorarão, e todos os que descem ao pó se prostrarão perante elle: e ninguem poderá reter viva a sua alma.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 Uma semente o servirá: será contada ao Senhor de geração em geração.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 Chegarão e annunciarão a sua justiça ao povo que nascer, porquanto elle o fez.
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.