< Salmos 122 >

1 Alegrei-me quando me disseram: Vamos á casa do Senhor.
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
2 Os nossos pés estão dentro das tuas portas, ó Jerusalem.
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
3 Jerusalem está edificada como uma cidade que é compacta,
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
4 Onde sobem as tribus, as tribus do Senhor, até o testemunho d'Israel, para darem graças ao nome do Senhor.
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
5 Pois ali estão os thronos do juizo, os thronos da casa de David.
A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
6 Orae pela paz de Jerusalem: prosperarão aquelles que te amam.
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
7 Haja paz dentro de teus muros, e prosperidade dentro dos teus palacios.
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
8 Por causa dos meus irmãos e amigos, direi: Paz esteja em ti.
Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
9 Por causa da casa do Senhor, nosso Deus, buscarei o teu bem.
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.

< Salmos 122 >