< Salmos 121 >
1 Levantarei os meus olhos para os montes, de onde vem a minha salvação.
Waƙar haurawa. Na tā da idanuna zuwa wajen tuddai, ta ina ne taimakona zai zo?
2 O meu soccorro vem do Senhor, que fez o céu e a terra.
Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
3 Não deixará vacillar o teu pé: aquelle que te guarda não tosquenejará.
Ba zai bari ƙafarka tă yi santsi ba, shi da yake tsaronka ba zai yi gyangyaɗi ba;
4 Eis-que não tosquenejará nem dormirá o guarda d'Israel.
tabbatacce, shi da yake tsaron Isra’ila ba ya gyangyaɗi ko barci.
5 O Senhor é quem te guarda: o Senhor é a tua sombra á tua direita.
Ubangiji yana tsaronka, Ubangiji ne inuwa a hannun damanka;
6 O sol não te molestará de dia nem a lua de noite.
rana ba za tă buge ka cikin yini ba balle wata da dare.
7 O Senhor te guardará de todo o mal: guardará a tua alma.
Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan masifa, zai tsare ranka;
8 O Senhor guardará a tua entrada e a tua saida, desde agora e para sempre.
Ubangiji zai kiyaye shigarka da fitarka yanzu da har abada kuma.