< Salmos 112 >

1 Louvae ao Senhor. Bemaventurado o homem que teme ao Senhor, que em seus mandamentos tem grande prazer.
Yabi Ubangiji. Mai albarka ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, wanda yakan sami farin ciki mai girma a umarnansa.
2 A sua semente será poderosa na terra: a geração dos rectos será abençoada.
’Ya’yansa za su zama manya a ƙasar; tsaran masu aikata gaskiya za su sami albarka.
3 Fazenda e riquezas haverá na sua casa, e a sua justiça permanece para sempre.
Wadata da arziki suna a cikin gidansa, adalcinsa zai dawwama har abada.
4 Aos justos nasce luz nas trevas: elle é piedoso, misericordioso e justo.
Ko a cikin duhu haske kan haskaka wa mai aikata gaskiya, mai alheri mai tausayi da kuma mai adalci.
5 O homem bom se compadece, e empresta: disporá as suas coisas com juizo.
Abu mai kyau zai zo masa shi da yake kyauta yake kuma ba da bashi hannu sake, shi da yake yin al’amuransa cikin gaskiya.
6 Na verdade que nunca será commovido: o justo estará em memoria eterna.
Tabbatacce ba zai taɓa jijjigu ba; za a tuna da mai adalci har abada.
7 Não temerá maus rumores: o seu coração está firme, confiando no Senhor.
Ba zai ji tsoron labari marar daɗi ba; zuciyarsa tsayayyiya ce, tana dogara ga Ubangiji.
8 O seu coração bem confirmado, elle não temerá, até que veja o seu desejo sobre os seus inimigos.
Zuciyarsa tana da kāriya, ba zai ji tsoro ba; a ƙarshe zai zama mai nasara a kan maƙiyansa.
9 Elle espalhou, deu aos necessitados: a sua justiça permanece para sempre, e a sua força se exaltará em gloria.
Ya rarraba kyautansa ga matalauta, adalcinsa zai dawwama har abada; za a ɗaga ƙahonsa sama da bangirma.
10 O impio o verá, e se entristecerá: rangerá com os dentes, e se consumirá o desejo dos impios perecerá.
Mugun mutum zai gani yă kuma yi fushi, zai ciza haƙora yă kuma lalace; sha’awace-sha’awacen mugaye za su zo ga ƙarshe.

< Salmos 112 >