< Provérbios 1 >

1 Proverbios de Salomão, filho de David, rei d'Israel;
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 Para se conhecer a sabedoria e a instrucção; para se entenderem as palavras da prudencia;
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 Para se receber a instrucção do entendimento, a justiça, o juizo, e a equidade;
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 Para dar aos simplice prudencia, e aos moços conhecimento e bom siso;
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 Para o sabio ouvir e crescer em doutrina, e o entendido adquirir sabios conselhos;
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 Para entender proverbios e a sua declaração: como tambem as palavras dos sabios, e as suas adivinhações.
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 O temor do Senhor é o principio da sciencia: os loucos desprezam a sabedoria e a instrucção.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 Filho meu, ouve a instrucção de teu pae, e não deixes a doutrina de tua mãe.
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 Porque diadema de graça serão para a tua cabeça, e colares para o teu pescoço.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 Filho meu, se os peccadores te attrahirem com afagos, não consintas.
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 Se disserem: Vem comnosco; espiemos o sangue; espreitemos o innocente sem razão;
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 Traguemol-os vivos, como a sepultura; e inteiros, como os que descem á cova; (Sheol h7585)
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
13 Acharemos toda a sorte de fazenda preciosa; encheremos as nossas casas de despojos;
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 Lança a tua sorte entre nós; teremos todos uma só bolsa.
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 Filho meu, não te ponhas a caminho com elles: desvia o pé das suas veredas;
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 Porque os seus pés correm para o mal, e se apressam a derramar sangue.
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 Na verdade debalde se estende a rede perante os olhos de toda a sorte d'aves.
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 E estes armam ciladas contra o seu proprio sangue; e as suas proprias vidas espreitam.
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 Assim são as veredas de todo aquelle que usa d'avareza: ella prenderá a alma de seus amos.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 A suprema sabedoria altamente clama de fóra: pelas ruas levanta a sua voz.
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 Nas encruzilhadas, em que ha tumultos, clama: ás entradas das portas, na cidade profere as suas palavras.
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 Até quando, ó simplices, amareis a simplicidade? e vós, escarnecedores, desejareis o escarneo? e vós, loucos, aborrecereis o conhecimento?
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 Tornae-vos á minha reprehensão: eis que abundantemente vos derramarei de meu espirito e vos farei saber as minhas palavras.
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 Porquanto clamei, e vós recusastes; estendi a minha mão, e não houve quem désse attenção;
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 Mas rejeitastes todo o meu conselho, e não quizestes a minha reprehensão.
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 Tambem eu me rirei na vossa perdição, e zombarei, vindo o vosso temor;
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 Vindo como a assolação o vosso temor, e vindo a vossa perdição como uma tormenta, sobrevindo-vos aperto e angustia.
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 Então a mim clamarão, porém eu não responderei; de madrugada me buscarão, porém não me acharão.
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 Porquanto aborreceram o conhecimento; e não elegeram o temor do Senhor;
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 Não consentiram ao meu conselho e desprezaram toda a minha reprehensão.
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 Assim que comerão do fructo do seu caminho, e fartar-se-hão dos seus proprios conselhos.
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 Porque o desvio dos simplices os matará, e a prosperidade dos loucos os destruirá.
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 Porém o que me der ouvidos habitará seguramente, e estará descançado do temor do mal
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”

< Provérbios 1 >