< Números 13 >

1 E fallou o Senhor a Moysés, dizendo:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Envia homens que espiem a terra de Canaan, que eu hei de dar aos filhos d'Israel; de cada tribu de seus paes enviareis um homem, sendo cada qual maioral entre elles.
“Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
3 E enviou-os Moysés do deserto de Paran, segundo o dito do Senhor; todos aquelles homens eram Cabeças dos filhos d'Israel.
Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
4 E estes são os seus nomes: Da tribu de Ruben, Sammua, filho de Saccur,
Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
5 Da tribu de Simeão Saphath, filho de Hori;
Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
6 Da tribu de Judah, Caleb, filho de Jefoné;
Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
7 Da tribu d'Issacar, Jigeal, filho de José;
Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
8 Da tribu d'Ephraim, Hosea, filho de Nun;
Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
9 Da tribu de Benjamin, Palti, filho de Raphu;
daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
10 Da tribu de Zebulon, Gaddiel, filho de Sodi;
Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
11 Da tribu de José, pela tribu de Manasseh, Gaddi filho de Susi;
Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
12 Da tribu de Dan, Ammiel, filho de Gemalli;
Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
13 Da tribu d'Aser, Sethur, filho de Michael;
Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
14 Da tribu de Naphtali, Nabbi, filho de Vophsi;
Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
15 Da tribu de Gad, Guel, filho de Machi.
Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
16 Estes são os nomes dos homens que Moysés enviou a espiar aquella terra: e a Hosea, filho de Nun, Moysés chamou Josué.
Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
17 Enviou-os pois Moysés a espiar a terra de Canaan: e disse-lhes: Subi por aqui para a banda do sul, e subi á montanha:
Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
18 E vêde que terra é, e o povo que n'ella habita; se é forte ou fraco; se pouco ou muito.
Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
19 E qual é a terra em que habita, se boa ou má: e quaes são as cidades em que habita; ou em arraiaes, ou em fortalezas.
Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
20 Tambem qual é a terra, se grossa ou magra: se n'ella ha arvores, ou não: e esforçae-vos, e tomae do fructo da terra. E eram aquelles dias os dias das primicias das uvas.
Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
21 Assim subiram, e espiaram a terra desde o deserto de Zín, até Rehob, á entrada de Hamath.
Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
22 E subiram para a banda do sul, e vieram até Hebron; e estavam ali Aiman, Sesai, e Talmai, filhos d'Enac: e Hebron foi edificada sete annos antes de Zoan no Egypto.
Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
23 Depois vieram até ao valle d'Escol, e d'ali cortaram um ramo de vide com um cacho d'uvas, o qual trouxeram dois homens sobre uma verga: como tambem das romãs e dos figos.
Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
24 Chamaram áquelle logar o valle d'Escol, por causa do cacho que d'ali cortaram os filhos de Israel.
Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
25 Depois tornaram-se d'espiar a terra, ao fim de quarenta dias.
A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
26 E caminharam, e vieram a Moysés e a Aarão, e a toda a congregação dos filhos de Israel no deserto de Paran, a Cades, e, tornando, deram-lhes conta a elles, e a toda a congregação, e mostraram-lhes o fructo da terra
Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
27 E contaram-lhe e disseram: Fomos á terra a que nos enviaste; e verdadeiramente mana leite e mel, e este é o fructo.
Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
28 O povo porém que habita n'essa terra é poderoso, e as cidades fortes e mui grandes; e tambem ali vimos os filhos d'Enac.
Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
29 Os amalequitas habitam na terra do sul; e os heteos, e os jebuseos, e os amorrheos habitam na montanha: e os cananeos habitam ao pé do mar, e pela ribeira do Jordão.
Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
30 Então Caleb fez calar o povo perante Moysés, e disse: Subamos animosamente, e possuamol-a em herança: porque certamente prevaleceremos contra ella.
Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
31 Porém os homens que com elle subiram disseram: Não poderemos subir contra aquelle povo, porque é mais forte do que nós.
Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
32 E infamaram a terra que tinham espiado para com os filhos d'Israel, dizendo: A terra, pelo meio da qual passamos a espiar, é terra que consome os seus moradores; e todo o povo que vimos no meio d'ella são homens de grande estatura.
Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
33 Tambem vimos ali gigantes, filhos d'Enac, descendentes dos gigantes: e eramos aos nossos olhos como gafanhotos, e assim tambem eramos aos seus olhos.
Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”

< Números 13 >