< Números 12 >

1 E fallaram Miriam e Aarão contra Moysés, por causa da mulher cushita, que tomara: porquanto tinha tomado a mulher cushita.
Miriyam da Haruna suka fara zargin Musa saboda matarsa’yar ƙasar Kush da ya aura.
2 E disseram: Porventura fallou o Senhor sómente por Moysés? não fallou tambem por nós? E o Senhor o ouviu.
Suka ce, “Ubangiji ya yi magana ta wurin Musa ne kaɗai? Ashe, bai yi magana ta wurinmu mu ma ba?” Ubangiji kuwa ya ji wannan.
3 E era o homem Moysés mui manso, mais de que todos os homens que havia sobre a terra.
(Musa kuwa mutum ne mai tawali’u ƙwarai, mafi tawali’u fiye da kowane mutum a duniya.)
4 E logo o Senhor disse a Moysés, e a Aarão, e a Miriam: Vós tres sahi á tenda da congregação. E sairam elles tres.
Nan da nan Ubangiji ya ce wa Musa, da Haruna da kuma Miriyam, “Ku fita ku tafi Tentin Sujada, dukanku uku.” Sai dukansu uku suka tafi.
5 Então o Senhor desceu na columna da nuvem, e se poz á porta da tenda: depois chamou a Aarão e a Miriam, e elles sairam ambos.
Sai Ubangiji ya sauko a cikin ginshiƙin girgije; ya tsaya a bakin ƙofar Tenti, ya kira Haruna da Miriyam. Sa’ad da su biyu suka gusa gaba,
6 E disse: Ouvi agora as minhas palavras; se entre vós houver propheta, Eu, o Senhor, em visão a elle me farei conhecer, ou em sonhos fallarei com elle.
sai ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa, “Duk lokacin da akwai annabin Ubangiji a cikinku, nakan bayyana kaina gare shi cikin wahayi, in yi magana da shi cikin mafarkai.
7 Não é assim com o meu servo Moysés que é fiel em toda a minha casa.
Amma ba haka nake magana da Musa bawana ba; na sa shi yă lura da dukan jama’ata Isra’ila.
8 Bocca a bocca fallo com elle, e de vista, e não por figuras; pois elle vê a similhança do Senhor: porque pois não tivestes temor de fallar contra o meu servo, contra Moysés?
Da shi nake magana fuska da fuska, a fili kuma, ba a kacici-kacici ba; yakan ga siffar Ubangiji. To, me ya sa ba ku ji tsoro ku yi magana a kan bawana Musa ba?”
9 Assim a ira do Senhor contra elles se accendeu; e foi-se.
Sai fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kansu, ya kuma rabu da su.
10 E a nuvem se desviou de sobre a tenda; e eis que Miriam era leprosa como a neve: e olhou Aarão para Miriam, e eis qua era leprosa.
Da girgijen ya tashi daga bisa Tentin, sai ga Miriyam tsaye, kuturwa, fari fat. Haruna kuwa ya juya wajenta ya ga ta kuturce;
11 Pelo que Aarão disse a Moysés: Ah senhor meu, ora não ponhas sobre nós este peccado, que fizemos loucamente, e com que havemos peccado.
sai Haruna ya ce wa Musa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka hukunta mu, gama zunubin da muka yi, mun yi ne cikin wauta.
12 Ora não seja ella como um morto, que saindo do ventre de sua mãe, a metade da sua carne já está consumida.
Kada ka sa ta zama kamar haifaffen mataccen jariri daga cikin mahaifiya wanda rabin jikin ruɓaɓɓe ne.”
13 Clamou pois Moysés ao Senhor, dizendo: O' Deus, rogo-te que a cures.
Saboda haka sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Allah, ina roƙonka ka warkar da ita!”
14 E disse o Senhor a Moysés: Se seu pae cuspira em seu rosto, não seria envergonhada sete dias? esteja fechada sete dias fóra do arraial, e depois a recolham.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata miyau a fuskarta, ashe, ba za tă ji kunya har kwana bakwai ba? A fitar da ita bayan sansani kwana bakwai; bayan haka za a iya dawo da ita.”
15 Assim Miriam esteve fechada fóra do arraial sete dias, e o povo não partiu, até que recolheram a Miriam.
Haka aka fitar da Miriyam bayan sansani kwana bakwai, mutane kuwa ba su ci gaba da tafiya ba sai da aka dawo da ita.
16 Porém depois o povo partiu de Hazeroth; e assentaram o arraial no deserto de Paran.
Bayan haka sai mutane suka bar Hazerot suka sauka a Hamadan Faran.

< Números 12 >