< Números 10 >
1 Fallou mais o Senhor a Moysés, dizendo:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Faze-te duas trombetas de prata: d'obra batida as farás: e te serão para a convocação da congregação, e para a partida dos arraiaes.
“Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
3 E, quando as tocarem ambas, então toda a congregação se congregará a ti á porta da tenda da congregação.
Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
4 Mas, quando tocar uma só, então a ti se congregarão os principes, os Cabeças dos milhares de Israel.
In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
5 Quando, retinindo, as tocardes, então partirão os arraiaes que alojados estão da banda do oriente.
Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
6 Mas, quando a segunda vez, retinindo, as tocardes, então partirão os arraiaes que se alojam da banda do sul: retinindo, as tocarão para as suas partidas.
A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
7 Porém, ajuntando a congregação, as tocareis; mas sem retinir.
In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
8 E os filhos d'Aarão, sacerdotes, tocarão as trombetas: e a vós serão por estatuto perpetuo nas vossas gerações.
“’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
9 E, quando na vossa terra sairdes a pelejar contra o inimigo, que vos aperta, tambem tocareis as trombetas retinindo, e perante o Senhor vosso Deus haverá lembrança de vós, e sereis salvos de vossos inimigos.
Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
10 Similhantemente, no dia da vossa alegria, e nas vossas solemnidades, e nos principios dos vossos mezes, tambem tocareis as trombetas sobre os vossos holocaustos, sobre os vossos sacrificios pacificos, e vos serão por memorial perante vosso Deus: Eu sou o Senhor vosso Deus.
Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
11 E aconteceu, no anno segundo, no segundo mez, aos vinte do mez, que a nuvem se alçou de sobre o tabernaculo da congregação.
A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
12 E os filhos d'Israel se partiram segundo as suas partidas do deserto de Sinai: e a nuvem parou no deserto de Paran.
Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
13 Assim partiram pela primeira vez segundo o dito do Senhor, pela mão de Moysés.
Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
14 Porque primeiramente partiu a bandeira do arraial dos filhos de Judah segundo os seus exercitos: e sobre o seu exercito estava Naasson, filho d'Amminadab.
Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
15 E sobre o exercito da tribu dos filhos d'Issacar, Nathanael, filho de Suhar.
Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
16 E sobre o exercito da tribu dos filhos de Zebulon, Eliab, filho de Helon.
Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
17 Então desarmaram o tabernaculo, e os filhos de Gerson e os filhos de Merari partiram, levando o tabernaculo.
Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
18 Depois partiu a bandeira do arraial de Ruben segundo os seus exercitos: e sobre o seu exercito estava Elizur, filho de Sedeur.
Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
19 E sobre o exercito da tribu dos filhos de Simeão, Selumiel, filho de Surisaddai.
Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
20 E sobre o exercito da tribu dos filhos de Gad, Eliasaph, filho de Dehuel.
Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
21 Então partiram os kohathitas, levando o sanctuario; e os outros levantaram o tabernaculo, entretanto que estes vinham.
Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
22 Depois partiu a bandeira do arraial dos filhos d'Ephraim segundo os seus exercitos: e sobre o seu exercito estava Elisama, filho d'Ammihud.
Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
23 E sobre o exercito da tribu dos filhos de Manasseh, Gamaliel, filho de Pedazur.
Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
24 E sobre o exercito da tribu dos filhos de Benjamin, Abidan, filho de Gideoni.
Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
25 Então partiu a bandeira do arraial dos filhos de Dan, fechando todos os arraiaes segundo os seus exercitos: e sobre o seu exercito estava Ahiezer, filho de Ammisaddai.
A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
26 E sobre o exercito da tribu dos filhos d'Aser, Pagiel, filho de Ochran.
Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
27 E sobre o exercito da tribu dos filhos de Naphtali, Ahira, filho d'Enan.
Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
28 Estas eram as partidas dos filhos d'Israel segundo os seus exercitos, quando partiam.
Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
29 Disse então Moysés a Hobab, filho de Reguel o midianita, sogro de Moysés: Nós caminhamos para aquelle logar, de que o Senhor disse: Vol-o darei: vae comnosco, e te faremos bem; porque o Senhor fallou bem sobre Israel.
Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
30 Porém elle lhe disse: Não irei; antes irei á minha terra e á minha parentela.
Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
31 E elle disse: Ora não nos deixes: porque tu sabes que nós nos alojamos no deserto; nos servirás d'olhos.
Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
32 E será que, vindo tu comnosco, e succedendo o bem, com que o Senhor nos fará bem, tambem nós te faremos bem.
In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
33 Assim partiram do monte do Senhor caminho de tres dias: e a arca do concerto do Senhor caminhou diante d'elles caminho de tres dias, para lhes buscar logar de descanço.
Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
34 E a nuvem do Senhor ia sobre elles de dia, quando partiam do arraial.
A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
35 Era pois que, partindo a arca, Moysés dizia: Levanta-te, Senhor, e dissipados sejam os teus inimigos, e fujam diante de ti os aborrecedores.
Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
36 E, pousando ella, dizia: Torna-te, ó Senhor, para os muitos milhares d'Israel.
Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”