< Marcos 13 >

1 E, saindo elle do templo, disse-lhe um dos seus discipulos: Mestre, olha que pedras, e que edificios!
da Yesu ke fita daga Haikalin, sai daya daga cikin almajirnsa ya ce masa “malam, dubi kyawawan duwatsunnan da kyawawan gine-ginnenan!”
2 E, respondendo Jesus, disse-lhe: Vês estes grandes edificios? Não ficará pedra sobre pedra que não seja derribada.
Ya ce masa, ka ga wadannan kyawawan gine- ginen? babu wani dutsen da za a bar shi akan dan'uwansa, da ba za a rushe shi ba.”
3 E, assentando-se elle no monte das Oliveiras, defronte do templo, Pedro, e Thiago, e João e André lhe perguntaram em particular:
Yana zaune a kan dutsen zaitun wanda yake kusa da Haikali, sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawus suka tambaye shi a asirce, suka ce.
4 Dize-nos, quando serão essas coisas, e que signal haverá quando todas essas coisas se houverem de cumprir.
Gaya mana yaushe za a yi wadannan abubuwa? mecece zata zama alamar faruwar wadanna abubuwa da zasu faru?''
5 E Jesus, respondendo-lhes, começou a dizer: Olhae que ninguem vos engane;
Yesu ya ce masu, “ku kula, kada kowa ya rudeku.
6 Porque muitos virão em meu nome, dizendo: Eu sou o Christo: e enganarão a muitos.
Da yawa za su zo da sunana, suna cewa nine shi, har su bad da mutane da yawa.
7 E, quando ouvirdes de guerras e de rumores de guerras, não vos turbeis; porque assim importa fazer-se; mas ainda não será o fim.
In kuka ji labarin yake- yake, da jita-jitarsu kada ku damu, wannan zai faru, amma karshen duniya bai gabato ba.
8 Porque se levantará nação contra nação, e reino contra reino, e haverá terremotos em diversos logares, e haverá fomes e alvoroços. Estas coisas serão o principio de dôres
Al'umma za ta tasarwa al'umma, mulki ya tasarwa mulki. Za a yi girgizar kasa awurare dabam-dabam, da kuma yunwa, amma fa dukkan wadanna abubuwan mafarin azaba ne.
9 Mas olhae por vós mesmos, porque vos entregarão aos concilios e ás synagogas; sereis açoitados, e sereis apresentados ante presidentes e reis, por amor de mim, para lhes servir de testemunho.
Amma, ku zauna a fadake. Don za su kai ku gaban majalisa. za a yi maku duka a cikin majami'u. Su kuma kai ku gaban masu mulki da sarakuna, saboda sunana, domin ku ba da shaida a gare su.
10 Mas importa que o evangelho se pregue primeiro entre todas as gentes.
Amma lallai sai an fara yi wa dukkan al, ummai bishara.
11 Quando pois vos conduzirem para vos entregarem, não estejaes solicitos d'antemão pelo que haveis de dizer; mas, o que vos fôr dado n'aquella hora, isso fallae; porque não sois vós os que fallaes, mas o Espirito Sancto.
Sa'ad da suka kai ku gaban shari'a suka mika ku, kada ku damu a wannan lokacin, za a baku abin da zaku fada, Amma duk abin da aka yi muku a wannn lokacin, shi za ku fada, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu mai tsarki ne.
12 E o irmão entregará á morte o irmão, e o pae o filho: e levantar-se-hão os filhos contra os paes, e os matarão.
Dan'uwa zai bada dan'uwarsa akashe shi, uba kuwa dansa. Yara kuma zasu tayar wa iyayensu har su sa akashe su.
13 E sereis aborrecidos por todos por amor do meu nome; mas quem perseverar até ao fim esse será salvo.
Za a ki ku saboda sunana, amma duk wanda ya jumre har karshe zai cetu.
14 Ora, quando vós virdes a abominação do assolamento, que foi predito, estando onde não deve estar (quem lê, entenda), então os que estiverem na Judea fujam para os montes.
Sa'adda kuka ga an kafa mummunan aikin sabo mai ban kyama a wurin da bai kamata ba (bari mai karatu ya fahimta), to, bari wadanda suke kasar Yahudiya, su gudu zuwa dutse.
15 E o que estiver sobre o telhado não desça para casa, nem entre a tomar coisa alguma de sua casa;
Wanda yake tudu kuma kada ya sauko ya shiga gida garin daukar wani abu.
16 E o que estiver no campo não volte atraz, para tomar o seu vestido.
Wanda yake gona kuma kada ya koma garin daukar mayafinsa.
17 Mas ai das gravidas, e das que criarem n'aquelles dias!
Amma, kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokacin.
18 Orae pois, para que a vossa fugida não succeda no inverno;
Ku yi addu, a kada abin ya faru da damina.
19 Porque n'aquelles dias haverá uma afflicção tal, qual nunca houve desde o principio da creação, que Deus creou, até agora, nem tão pouco haverá
A lokacin za ayi wata matsanaciyar wahala, wadda bata taba faruwa ba, tun farkon halittar da Allah ya yi har zuwa yau, ba kuwa za a taba yi ba har abada.
20 E, se o Senhor não abreviasse aquelles dias, nenhuma carne se salvaria; mas, por causa dos escolhidos que escolheu, abreviou aquelles dias.
In da ba ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba Dan adam din zai tsira. Amma saboda zabbabunan da ya zaba, ya rage kwanakin.
21 E então, se alguem vos disser: Eis aqui está o Christo: ou, Eil-o ali está: não o acrediteis.
To, in wani ya ce maku, kun ga Almasihu nan!' ko, 'kun gan shi can, kada ku gaskata.
22 Porque se levantarão falsos christos, e falsos prophetas, e farão signaes e prodigios, para enganarem, se fôr possivel, até os escolhidos.
Gama almasihan karya, da annabawan karya zasu bayyana kuma, zasu yi abubuwan al'ajibai masu ban mamaki.
23 Mas vós vede; eis que d'antemão vos tenho dito tudo.
Amma ku zauna a fadake, Na dai fada maku wadannan abubuwan kafin lokacin.
24 Ora, n'aquelles dias, depois d'aquella afflicção, o sol se escurecerá, e a lua não dará o seu resplendor,
Amma, bayan matsanaciyar wahalannan, rana zata duhunta, wata kuma ba zai bada haske ba.
25 E as estrellas cairão do céu, e as forças que estão nos céus serão abaladas.
Taurari za su fado daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.
26 E então verão vir o Filho do homem nas nuvens, com grande poder e gloria.
Sa' annan zasu ga Dan mutum na zuwa a cikin gajimare, da iko mai girma da daukaka.
27 E então enviará os seus anjos, e ajuntará os seus escolhidos, desde os quatro ventos, da extremidade da terra até á extremidade do céu.
Zai aiko da mala'ikunsa su tattaro zabbabunsa daga kusuwoyi hudu na duniya(watau Gabas da Yamma, kudu da Arewa) har zuwa karshen sama.
28 Aprendei pois a parabola da figueira: Quando já o seu ramo se torna tenro, e brota folhas, bem sabeis que já está proximo o verão.
“Ku yi koyi da itacen baure. Da zarar rassansa sun fara taushi yana kuma fitar da toho, kun san damina ta yi kusa ke nan.
29 Assim tambem vós, quando virdes succederem estas coisas, sabei que já está junto ás portas.
Sa'adda kuka ga wadannan abubuwa suna faruwa, ku dai sani ya kusato, a bakin kofa ma ya ke.
30 Na verdade vos digo que não passará esta geração, até que todas estas coisas aconteçam.
Hakika ina gaya maku, zamanin nan ba zai shude ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
31 Passará o céu e a terra, mas as minhas palavras não passarão.
Sararin sama da kasa za su shude, amma maganata ba za ta shude ba.
32 Porém d'aquelle dia e hora ninguem sabe, nem os anjos que estão no céu, nem o Filho, senão o Pae
Amma wannan rana ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai dai Uban kadai.
33 Olhae, vigiae e orae; porque não sabeis quando chegará o tempo.
Ku kula, ku zauna a fadake, kuna addu'a don baku san ranar da lokacin zai yi ba.
34 Como o homem, que, partindo para fóra da terra, deixou a sua casa, e deu auctoridade aos seus servos, e a cada um a sua obra, e mandou ao porteiro que vigiasse;
Kamar yadda mutum mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta bayinsa kan gidansa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai gadi ya zauna a fadake.
35 Vigiae pois, porque não sabeis quando virá o senhor da casa; se á tarde, se á meia noite, se ao cantar do gallo, se pela manhã,
To, ku zauna a fadake don ba ku san lokacin da maigidan zai zo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne.
36 Para que não venha de improviso, e vos ache dormindo.
Kada ya zo ba zato, ya samu kuna barci.
37 E as coisas que vos digo digo-as a todos: Vigiae.
Abinda na gaya maku, ina gaya wa kowa, shine ku zauna a fadake!”

< Marcos 13 >