< Josué 13 >
1 Era, porém, Josué já velho, entrado em dias; e disse-lhe o Senhor: Já estás velho, entrado em dias; e ainda muitissima terra ficou para possuir.
Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
2 A terra que fica de resto é esta: todos os termos dos philisteos, e toda a Gesuri;
“Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
3 Desde Sihor, que está defronte do Egypto, até ao termo de Ekron para o norte, que se conta ser dos cananeos: cinco principes dos philisteos, o gazeo, e o asdodeo, o ascalonita, o getheo, e o ekroneo, e os aveos;
Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
4 Desde o sul, toda a terra dos cananeos, e Meara, que é dos sidoneos; até Aphek: até ao termo dos amorrheos;
Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
5 Como tambem a terra dos gibleos, e todo o Libano para o nascente do sol, desde Baal-gad, ao pé do monte Hermon, até á entrada d'Hamath;
da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
6 Todos os que habitam nas montanhas desde o Libano até Misrephoth-main, todos os sidoneos; eu os lançarei de diante dos filhos de Israel: tão sómente faze que a terra caia a Israel em sorte por herança, como já t'o tenho mandado.
“Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
7 Reparte pois agora esta terra por herança ás nove tribus e á meia tribu de Manasseh;
ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
8 Com quem os rubenitas e os gaditas já receberam a sua heranca; a qual lhes deu Moysés d'além do Jordão para o oriente; como já lhes tinha dado Moysés, servo do Senhor,
Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
9 Desde Aroer, que está á borda do ribeiro d'Arnon, e a cidade que está no meio do valle, e toda a campina de Medeba até Dibon;
Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
10 E todas as cidades de Sehon, rei dos amorrheos, que reinou em Hesbon, até ao termo dos filhos d'Ammon;
da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
11 E Gilead, e o termo dos gesureos, e dos maacateos, e todo o monte Hermon, e toda a Basan até Salcha:
Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
12 Todo o reino d'Og em Basan, que reinou em Astaroth e em Edrei; este ficou do resto dos gigantes que Moysés feriu e expelliu.
wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
13 Porém os filhos de Israel não expelliram os gesureos, nem os maacateos; antes Gesur e Maacath habitaram no meio de Israel até ao dia de hoje.
Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
14 Tão sómente á tribu de Levi não deu herança: os sacrificios queimados do Senhor Deus de Israel são a sua herança, como já lhe tinha dito.
Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
15 Assim Moysés deu á tribu dos filhos de Ruben, conforme as suas familias.
Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
16 E foi o seu termo desde Aroer, que está á borda do ribeiro d'Arnon, e a cidade que está no meio do valle, e toda a campina até Medeba;
Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
17 Hesbon e todas as suas cidades, que estão na campina: Dibon, e Bamoth-baal, e Beth-baal-meon;
zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
18 E Jahsa, e Kedemoth, e Mephaat;
Yahza, Kedemot, Mefa’at,
19 E Kiriathaim, e Sibma, e Zereth, e Hassahar, no monte do valle;
Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
20 E Beth-peor, e Asdoth-pisga, e Beth-jesimoth;
Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
21 E todas as cidades da campina, e todo o reino de Sehon, rei dos amorrheos, que reinou em Hesbon, a quem Moysés feriu, como tambem aos principes de Midian, Evi, e Rekem, e Sur, e Hur, e Reba, principes de Sehon, moradores da terra.
dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
22 Tambem os filhos de Israel mataram á espada a Balaão, filho de Beor, o adivinho, como os mais que por elles foram mortos.
Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
23 E foi o termo dos filhos de Ruben o Jordão e o seu termo; esta é a herança dos filhos de Ruben, segundo as suas familias, as cidades, e as suas aldeias.
Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
24 E deu Moysés á tribu de Gad, aos filhos de Gad, segundo as suas familias.
Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
25 E foi o seu termo Jaezer, e todas as cidades de Gilead, e metade da terra dos filhos d'Ammon, até Aroer, que está defronte de Rabba;
Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
26 E desde Hesbon até Ramath-mispe, e Bethonim: e desde Mahanaim até ao termo de Debir;
da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
27 E no valle Beth-aram, e Beth-nimra, e Succoth, e Saphon, que ficara do resto do reino do rei de Sehon em Hesbon, o Jordão e o seu termo, até á extremidade do mar de Cinnereth d'além do Jordão para o oriente.
kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
28 Esta é a herança dos filhos de Gad, segundo as suas familias, as cidades e as suas aldeias.
Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
29 Deu tambem Moysés herança á meia tribu de Manasseh, que ficou á meia tribu dos filhos de Manasseh, segundo as suas familias,
Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
30 De maneira que o seu termo foi desde Mahanaim, todo o Basan, todo o reino d'Og, rei de Basan, e todas as aldeias de Jair, que estão em Basan, sessenta cidades,
Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
31 E metade de Gilead, e Astaroth, e Edrei, cidades do reino d'Og, em Basan, aos filhos de Machir, filho de Manasseh, a saber, á metade dos filhos de Machir, segundo as suas familias.
da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
32 Isto é o que Moysés repartiu em herança nas campinas de Moab, d'além do Jordão de Jericó para o oriente.
Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
33 Porém á tribu de Levi Moysés não deu herança: o Senhor Deus de Israel é a sua herança, como já lhe tinha dito.
Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.