< 35 >

1 Respondeu mais Elihu e disse:
Sai Elihu ya ce,
2 Tens por direito dizeres: Maior é a minha justiça do que a de Deus?
“Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
3 Porque disseste: De que te serviria elle? ou de que mais me aproveitarei do que do meu peccado?
Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
4 Eu te farei resposta, a ti e aos teus amigos comtigo.
“Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
5 Attenta para os céus, e vê; e contempla as mais altas nuvens, que são mais altas do que tu
Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
6 Se peccares, que effectuarás contra elle? se as tuas transgressões se multiplicarem, que lhe farás.
In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
7 Se fôres justo, que lhe darás? ou que receberá da tua mão?
In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
8 A tua impiedade damnaria outro tal como tu; e a tua justiça aproveitaria ao filho do homem.
Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
9 Por causa da grandeza da oppressão fazem clamar aos opprimidos: exclamam por causa do braço dos grandes.
“Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
10 Porém ninguem diz: Onde está Deus que me fez, que dá psalmos na noite.
Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
11 Que nos faz mais doutos do que os animaes da terra, e nos faz mais sabios do que as aves dos céus.
wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
12 Ali clamam, porém elle não responde, por causa da arrogancia dos maus.
Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
13 Certo é que Deus não ouvirá a vaidade, nem attentará para ella o Todo-poderoso.
Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
14 E quanto ao que disseste, que o não verás: juizo ha perante elle; por isso espera n'elle.
Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
15 Mas agora, ainda que a ninguem a sua ira visitasse, nem advertisse muito na multidão dos peccadores:
Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
16 Logo Job em vão abriu a sua bocca, e sem sciencia multiplicou palavras.
Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”

< 35 >