< 30 >

1 Porém agora se riem de mim os de menos edade do que eu, cujos paes eu teria desdenhado de pôr com os cães do meu rebanho.
“Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
2 De que tambem me serviria a força das suas mãos? já de velhice se tinham esgotado n'elles.
Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
3 De mingua e fome andavam sós, e recolhiam-se para os logares seccos, tenebrosos, assolados e desertos.
Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
4 Apanhavam malvas junto aos arbustos, e o seu mantimento eram as raizes dos zimbros.
A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
5 Do meio dos homens foram expulsos, e gritavam contra elles, como contra o ladrão:
An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
6 Para habitarem nos barrancos dos valles, e nas cavernas da terra e das rochas.
An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
7 Bramavam entre os arbustos, e ajuntavam-se debaixo das ortigas.
Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
8 Eram filhos de doidos, e filhos de gente sem nome, e da terra foram expulsos.
Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
9 Porém agora sou a sua canção, e lhes sirvo de rifão.
“Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
10 Abominam-me, e fogem para longe de mim, e do meu rosto não reteem o seu escarro.
Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
11 Porque Deus desatou o meu cordão, e me opprimiu, pelo que sacudiram de si o freio perante o meu rosto.
Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
12 Á direita se levantam os moços; empurram os meus pés, e preparam contra mim os seus caminhos de destruição.
A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
13 Desbarataram-me o meu caminho: promovem a minha miseria: não teem ajudador.
Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
14 Veem contra mim como por uma grande brecha, e revolvem-se entre a assolação.
Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
15 Sobrevieram-me pavores; como vento perseguem a minha honra, e como nuvem passou a minha felicidade.
Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
16 E agora derrama-se em mim a minha alma: os dias da afflicção se apoderaram de mim.
“Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
17 De noite se me traspassam os meus ossos, e os pulsos das minhas veias não descançam.
Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
18 Pela grandeza da força das dôres se demudou o meu vestido, e elle como o cabeção da minha tunica me cinge.
A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
19 Lançou-me na lama, e fiquei similhante ao pó e á cinza.
Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
20 Clamo a ti, porém tu não me respondes: estou em pé, porém para mim não attentas.
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
21 Tornaste-te a ser cruel contra mim: com a força da tua mão resistes violentamente.
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
22 Levantas-me sobre o vento, fazes-me cavalgar sobre elle, e derretes-me o ser.
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
23 Porque eu sei que me levarás á morte e á casa do ajuntamento determinado a todos os viventes.
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
24 Porém não estenderá a mão para o montão de terra, se houve clamor n'elles contra mim na sua desventura.
“Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
25 Porventura, não chorei sobre aquelle que estava afflicto? ou não se angustiou a minha alma pelo necessitado?
Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
26 Todavia aguardando eu o bem, então me veiu o mal, e esperando eu a luz, veiu a escuridão.
Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
27 As minhas entranhas ferveram e não estão quietas: os dias da afflicção me surprehenderam.
Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
28 Denegrido ando, porém não do sol, e, levantando-me na congregação, clamo por soccorro.
Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
29 Irmão me fiz dos dragões, e companheiro dos abestruzes.
Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
30 Ennegreceu-se a minha pelle sobre mim, e os meus ossos estão queimados do calor.
Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
31 Pelo que se trocou a minha harmonia em lamentação, e o meu orgão em voz dos que choram.
Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.

< 30 >