< Jó 17 >
1 O meu espirito se vae corrompendo, os meus dias se vão apagando, e tenho perante mim as sepulturas.
Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
2 Porventura não estão zombadores comigo? e os meus olhos não passam a noite chorando pelas suas amarguras?
Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
3 Promette agora, e dá-me um fiador para comtigo: quem ha que me dê a mão?
“Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
4 Porque aos seus corações encobriste o entendimento, pelo que não os exaltarás.
Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
5 O que lisongeando falla aos amigos tambem os olhos de seus filhos desfallecerão.
In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
6 Porém a mim me poz por um proverbio dos povos, de modo que já sou uma abominação perante o rosto de cada um.
“Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
7 Pelo que já se escureceram de magoa os meus olhos, e já todos os meus membros são como a sombra:
Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
8 Os rectos pasmarão d'isto, e o innocente se levantará contra o hypocrita.
Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
9 E o justo seguirá o seu caminho firmemente, e o puro de mãos irá crescendo em força.
Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
10 Mas, na verdade, tornae todos vós, e vinde cá; porque sabio nenhum acho entre vós.
“Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
11 Os meus dias passam, os meus propositos se quebraram, os pensamentos do meu coração.
Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
12 Trocaram o dia em noite; a luz está perto do fim, por causa das trevas.
Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
13 Se eu esperar, a sepultura será a minha casa; nas trevas estenderei a minha cama. (Sheol )
In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol )
14 Á corrupção clamo: Tu és meu pae; e aos bichos: Vós sois minha mãe e minha irmã.
In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
15 Onde pois estaria agora a minha esperança? emquanto á minha esperança, quem a poderá ver
To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
16 As barras da sepultura descerão quando juntamente no pó haverá descanço. (Sheol )
Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol )