< Gênesis 25 >
1 E Abrahão tomou outra mulher; e o seu nome era Ketura;
Ibrahim ya auro wata mace, mai suna Ketura.
2 E pariu-lhe Zimran, e Joksan, e Medan, e Midian, e Jisbac, e Shuah.
Ta haifa masa Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa.
3 E Joksan gerou Seba e Dedan: e os filhos de Dedan foram Assurim, e Letusim e Leummim.
Yokshan shi ne mahaifin Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Ashur, da mutanen Letush, da kuma mutanen Lewummin.
4 E os filhos de Midian foram Epha, e Epher, e Henoch, e Abidah, e Eldah: estes todos foram filhos de Ketura.
’Ya’yan Midiyan maza su ne, Efa, Efer, Hanok, Abida, da kuma Elda’a. Dukan waɗannan zuriyar Ketura ce.
5 Porém Abrahão deu tudo o que tinha a Isaac;
Ibrahim ya bar wa Ishaku kome da ya mallaka.
6 Mas aos filhos das concubinas que Abrahão tinha, deu Abrahão presentes, e, vivendo elle ainda, despediu-os do seu filho Isaac, ao oriente, para a terra oriental.
Amma yayinda Ibrahim yake da rai, ya ba wa’ya’yan ƙwarƙwaransa maza kyautai, ya kuma sallame su daga ɗansa Ishaku zuwa ƙasashen gabas.
7 Estes pois são os dias dos annos da vida de Abrahão, que viveu cento e setenta e cinco annos.
Duka-duka, Ibrahim ya yi shekara ɗari da saba’in da biyar.
8 E Abrahão expirou e morreu em boa velhice, velho e farto de dias: e foi congregado ao seu povo;
Sa’an nan Ibrahim ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu da kyakkyawar tsufa, tsoho da kuma shekaru masu yawa; aka kuma tara shi ga mutanensa.
9 E sepultaram-o Isaac e Ishmael, seus filhos, na cova de Machpelah, no campo d'Ephron, filho de Zohar hetheo, que estava em frente de Mamre,
’Ya’yansa maza kuwa Ishaku da Ishmayel suka binne shi cikin kogon Makfela, kusa da Mamre, a cikin filin Efron ɗan Zohar mutumin Hitti,
10 O campo que Abrahão comprara aos filhos de Heth. Ali está sepultado Abrahão, e Sarah sua mulher.
filin da Ibrahim ya saya daga Hittiyawa. A nan aka binne Ibrahim tare da matarsa Saratu.
11 E aconteceu depois da morte de Abrahão, que Deus abençoou a Isaac seu filho; e habitava Isaac junto ao poço Lahai-roi.
Bayan rasuwar Ibrahim, Allah ya albarkaci ɗansa Ishaku wanda a lokacin yana zama kusa da Beyer-Lahai-Royi.
12 Estas porém são as gerações de Ishmael filho de Abrahão, que a serva de Sarah, Hagar Egypcia, pariu a Abrahão.
Waɗannan su ne zuriyar Ishmayel ɗan Ibrahim, wanda Hagar mutuniyar Masar, baranyar Saratu, ta haifa wa Ibrahim.
13 E estes são os nomes dos filhos de Ishmael pelos seus nomes, segundo as suas gerações: o primogenito de Ishmael era Nebajoth, depois Kedar, e Abdeel, e Mibsam,
Ga jerin sunayen’ya’yan Ishmayel maza bisa ga haihuwarsu, Nebayiwot ɗan farin Ishmayel, Kedar, Adbeyel, Mibsam,
14 E Misma, e Duma, e Massa,
Mishma, Duma, Massa,
15 Hadar, e Tema, Jetur, Nafis, e Kedma.
Hadad, Tema, Yetur, Nafish da Kedema.
16 Estes são os filhos de Ishmael, e estes são os seus nomes pelas suas villas e pelos seus castellos: doze principes segundo as suas familias.
Waɗannan su ne’ya’yan Ishmayel maza, waɗanda kuma suke sunayen kabilu goma sha biyu masu mulki bisa ga wuraren zamansu da sansaninsu.
17 E estes são os annos da vida de Ishmael, cento e trinta e sete annos; e elle expirou, e morreu, e foi congregado ao seu povo.
Duka-duka Ishmayel ya yi shekara ɗari da talatin da bakwai; sai ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuma mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa.
18 E habitaram desde Havila até Sur, que está em frente do Egypto, indo para Assur; e fez o seu assento diante da face de todos os seus irmãos.
Zuriyarsa sun zauna tsakanin Hawila ne da Shur, wanda yake kusa da gabashin iyakar Masar wajen Asshur. Sun yi zaman rikici da dukan sauran’yan’uwansu.
19 E estas são as gerações de Isaac, filho de Abrahão: Abrahão gerou a Isaac:
Waɗannan su ne zuriyar Ishaku ɗan Ibrahim. Ibrahim ya haifi Ishaku,
20 E era Isaac da edade de quarenta annos, quando tomou a Rebecca, filha de Bethuel arameo de Paddan-aram, irmã de Labão arameo, por sua mulher.
Ishaku yana da shekara arba’in sa’ad da ya auri Rebeka’yar Betuwel, mutumin Aram, daga Faddan Aram,’yar’uwar Laban mutumin Aram.
21 E Isaac orou instantemente ao Senhor por sua mulher, porquanto era esteril; e o Senhor ouviu as suas orações, e Rebecca sua mulher concebeu.
Ishaku ya yi addu’a ga Ubangiji a madadin matarsa, saboda ba ta haihuwa. Ubangiji ya amsa addu’arsa, matarsa Rebeka kuwa ta yi ciki.
22 E os filhos luctavam dentro d'ella; então disse: Se assim é, porque sou eu assim? E foi-se a perguntar ao Senhor.
Jariran suka kama kokawa da juna a cikinta, sai ta ce, “Me ya sa wannan yake faruwa da ni?” Saboda haka ta tafi don ta nemi nufin Ubangiji.
23 E o Senhor lhe disse: Duas nações ha no teu ventre, e dois povos se dividirão das tuas entranhas, e um povo-será mais forte do que o outro povo, e o maior servirá ao menor.
Ubangiji ya ce mata, “Al’ummai biyu suna a cikin mahaifarki mutum biyu da za ki haifa, za su rabu da juna, ɗayan zai fi ɗayan ƙarfi, babban kuma zai bauta wa ƙaramin.”
24 E cumprindo-se os seus dias para parir, eis gemeos no seu ventre.
Da lokaci ya yi da za tă haihu, sai ga’yan biyu maza a mahaifarta.
25 E saiu o primeiro ruivo e todo como um vestido cabelludo; por isso chamaram o seu nome Esaú.
Wanda ya fara fita ja ne, dukan jikinsa kuwa kamar riga mai gashi. Don haka aka sa masa suna Isuwa.
26 E depois saiu o seu irmão, agarrada sua mão ao calcanhar de Esaú; por isso se chamou o seu nome Jacob. E era Isaac da edade de sessenta annos quando os gerou.
Bayan wannan, ɗan’uwansa ya fito, da hannunsa yana riƙe da ɗiɗɗigen Isuwa; don haka aka sa masa suna Yaƙub. Ishaku yana da shekara sittin, lokacin da Rebeka ta haife su.
27 E cresceram os meninos, e Esaú foi varão perito na caça, varão do campo; mas Jacob era varão simples, habitando em tendas.
Yaran suka yi girma, Isuwa kuwa ya zama riƙaƙƙen maharbi, mutumin jeji, yayinda Yaƙub, shiru-shiru ne mai son zama a tentuna.
28 E amava Isaac a Esaú, porque a caça era de seu gosto, mas Rebecca amava a Jacob.
Ishaku, mai son ci naman jeji, ya ƙaunaci Isuwa, amma Rebeka ta ƙaunaci Yaƙub.
29 E Jacob cozera um guisado; e veiu Esaú do campo, e estava elle cançado:
Wata rana sa’ad da Yaƙub yana dafa fate. Isuwa ya shigo daga jeji, da yunwa sosai.
30 E disse Esaú a Jacob: Deixa-me, peço-te, sorver d'esse guisado vermelho, porque estou cançado. Por isso se chamou o seu nome Edom.
Ya ce wa Yaƙub, “Ina roƙonka, ka ɗan ɗiba mini faten nan! Ina fama da yunwa!” (Shi ya sa aka kira shi Edom.)
31 Então disse Jacob: Vende-me hoje a tua primogenitura.
Yaƙub ya amsa ya ce, “Ka fara sayar mini da matsayinka na ɗan fari tukuna.”
32 E disse Esaú: Eis que estou a ponto de morrer, e para que me servirá logo a primogenitura?
Isuwa ya ce, “Duba, ina gab da mutuwa, me matsayina na ɗan fari zai yi mini?”
33 Então disse Jacob: Jura-me hoje. E jurou-lhe e vendeu a sua primogenitura a Jacob.
Amma Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini tukuna.” Don haka ya rantse masa, ya sayar da matsayinsa na ɗan fari ga Yaƙub.
34 E Jacob deu pão a Esaú e o guisado das lentilhas; e comeu, e bebeu, e levantou-se, e foi-se. Assim desprezou Esaú a sua primogenitura.
Sa’an nan Yaƙub ya ba wa Isuwa burodi da ɗan miyan lansir. Ya ci, ya sha, sa’an nan ya tashi ya tafi. Ta haka Isuwa ya yi banza da matsayinsa na ɗan fari.