< Gênesis 15 >

1 Depois d'estas coisas veiu a palavra do Senhor a Abrão em visão, dizendo: Não temas, Abrão, eu sou o teu escudo, o teu grandissimo galardão.
Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
2 Então disse Abrão: Senhor Jehovah, que me has de dar, pois ando sem filhos, e o mordomo da minha casa é o damasceno Elieser?
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
3 Disse mais Abrão: Eis que me não tens dado semente, e eis que um nascido na minha casa será o meu herdeiro.
Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
4 E eis que veiu a palavra do Senhor a elle, dizendo: Este não será o teu herdeiro; mas aquelle que de tuas entranhas sair, este será o teu herdeiro.
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
5 Então o levou fóra, e disse: Olha agora para os céus, e conta as estrellas, se as podes contar. E disse-lhe: Assim será a tua semente.
Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
6 E creu elle no Senhor, e imputou-lhe isto por justiça.
Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
7 Disse-lhe mais: Eu sou o Senhor, que te tirei de Ur dos Chaldeus, para dar-te a ti esta terra, para herdal-a.
Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
8 E disse elle: Senhor Jehovah, como saberei que hei-de herdal-a?
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
9 E disse-lhe: Toma-me uma bezerra de tres annos, e uma cabra de tres annos, e um carneiro de tres annos, uma rola, e um pombinho.
Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
10 E trouxe-lhe todos estes, e partiu-os pelo meio, e poz cada parte d'elles em frente da outra; mas as aves não partiu.
Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
11 E as aves desciam sobre os cadaveres; Abrão, porém, as enxotava.
Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
12 E pondo-se o sol, um profundo somno caiu sobre Abrão; e eis que grande espanto e grande escuridão caiu sobre elle.
Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
13 Então disse a Abrão: Saibas, de certo, que peregrina será a tua semente em terra que não é sua, e servil-os-hão; e affligil-os-hão quatrocentos annos;
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
14 Mas tambem eu julgarei a gente, a qual servirão, e depois sairão com grande fazenda.
Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
15 E tu irás a teus paes em paz: em boa velhice serás sepultado.
Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
16 E a quarta geração tornará para cá; porque a medida da injustiça dos Amoreos não está ainda cheia.
A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
17 E succedeu que, posto o sol, houve escuridão: e eis um forno de fumo, e uma tocha de fogo, que passou por aquellas metades.
Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
18 N'aquelle mesmo dia fez o Senhor um concerto com Abrão, dizendo: Á tua semente tenho dado esta terra, desde o rio Egypto até ao grande rio Euphrates;
A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
19 E o Keneo, e o Kenezeo, e o Kadmoneo,
ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
20 E o Hetheo, e o Pereseo, e os Rephains,
Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
21 E o Amoreo, e o Cananeo, e o Girgaseo, e o Jebuseo.
Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”

< Gênesis 15 >