< Amós 1 >
1 As palavras de Amós, que era d'entre os pastores de Tecoa, as quaes viu sobre Israel, nos dias de Uzias, rei de Judah, e nos dias de Jeroboão, filho de Joás, rei de Israel, dois annos antes do terremoto.
Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
2 E disse: O Senhor bramará de Sião, e de Jerusalem dará a sua voz: as habitações dos pastores prantearão, e seccar-se-ha o cume do Carmelo.
Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
3 Assim diz o Senhor: Por tres transgressões de Damasco, e por quatro, não o afastarei, porque trilharam a Gilead com trilhos de ferro.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
4 Por isso porei fogo á casa de Hazael, e consumirá os palacios de Benhadad.
zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
5 E quebrarei o ferrolho de Damasco, e exterminarei o morador de Biqueat-aven, e ao que tem o sceptro de Beth-eden; e o povo da Syria será levado em captiveiro a Kir, diz o Senhor.
Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
6 Assim diz o Senhor: Por tres transgressões de Gaza, e por quatro, não o afastarei, porque levaram em captiveiro todos os captivos para os entregarem a Edom.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
7 Por isso porei fogo ao muro de Gaza, que consumirá os seus palacios.
Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
8 E exterminarei o morador de Asdod, e o que tem o sceptro de Ascalon, e tornarei a minha mão contra Ecron; e o resto dos philisteos perecerá, diz o Senhor Jehovah.
Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Assim diz o Senhor: Por tres transgressões de Tyro, e por quatro, não o afastarei, porque entregaram todos os captivos a Edom, e não se lembraram da alliança dos irmãos.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
10 Por isso porei fogo ao muro de Tyro, que consumirá os seus palacios.
zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
11 Assim diz o Senhor: Por tres transgressões de Edom, e por quatro, não o afastarei, porque perseguiu a seu irmão á espada, e corrompeu as suas misericordias; e a sua ira despedaça eternamente, e retem a sua indignação para sempre
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
12 Por isso porei fogo a Teman, que consumirá os palacios de Bozra.
Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
13 Assim diz o Senhor: Por tres transgressões dos filhos de Ammon, e por quatro, não o afastarei, porque fenderam as gravidas de Gilead, para dilatarem os seus termos.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
14 Por isso porei fogo ao muro de Rabba, que consumirá os seus palacios, com alarido no dia da batalha, com tempestade no dia da tormenta.
Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
15 E o seu rei irá para o captiveiro, elle e os seus principes juntamente, diz o Senhor.
Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.