< 2 Samuel 8 >
1 E Succedeu depois d'isto que David feriu os philisteos, e os sujeitou: e David tomou a Metheg-ammah das mãos dos philisteos.
Ana nan, sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar, ya kuma ƙwace ƙasar Meteg Amma daga hannun Filistiyawa.
2 Tambem feriu os moabitas, e os mediu com cordel, fazendo-os deitar por terra, e os mediu com dois cordeis para os matar, e com um cordel inteiro para os deixar em vida: ficaram assim os moabitas por servos de David, trazendo presentes.
Haka kuma Dawuda ya ci Mowabawa. Ya sa suka kwanta a ƙasa, ya kuma auna su da igiya. Kowane awo biyu ya sa a kashe su, amma awo na uku sai yă sa a bar su da rai. Saboda haka Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka kuma kawo masa haraji.
3 Feriu tambem David a Hadadezer, filho de Rechob, rei de Zoba, indo elle a virar a sua mão para o rio Euphrates.
Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba. Wannan ya faru a lokacin da Hadadezer yake kan hanyarsa zuwa Kogin Yuferites don yă sāke mai da wurin a ƙarƙashin ikonsa.
4 E tomou-lhe David mil e seiscentos cavalleiros e vinte mil homens de pé: e David jarretou a todos os cavallos dos carros, e reservou d'elles cem carros.
Dawuda ya kame keken yaƙinsa guda dubu, mahayan keken yaƙinsa dubu bakwai, da sojojin ƙasa dubu ashirin. Ya yayyanke agaran dawakan duka amma ya bar dawakai kekunan yaƙi ɗari.
5 E vieram os syros de Damasco a soccorrer a Hadadezer, rei de Zoba: porém David feriu dos syros vinte e dois mil homens.
Sa’ad da Arameyawan Damaskus suka zo don su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe dubu ashirin da biyunsu.
6 E David poz guarnições em Syria de Damasco, e os syros ficaram por servos de David, trazendo presentes: e o Senhor guardou a David por onde quer que ia.
Ya ajiye ƙungiyoyi sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus, Arameyawa kuwa suka zama bayinsa, suka biya shi haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
7 E David tomou os escudos de oiro que havia com os servos de Hadadezer, e os trouxe a Jerusalem.
Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariya na shugabannin sojojin Hadadezer ya kawo Urushalima.
8 Tomou mais o rei David uma quantidade mui grande de bronze de Betah e de Berothai, cidades de Hadadezer.
Daga Teba da Berotai, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Sarki Dawuda ya kwashe tagulla masu yawan gaske.
9 Ouvindo então Toi, rei de Hamath, que David ferira a todo o exercito de Hadadezer,
Da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer,
10 Mandou Toi seu filho Joram ao rei David, para lhe perguntar como estava, e para lhe dar os parabens por haver pelejado contra Hadadezer, e por o haver ferido (porque Hadadezer de continuo fazia guerra a Toi); e na sua mão trazia vasos de prata, e vasos de oiro, e vasos de bronze,
sai ya aiki ɗansa Yoram wurin Sarki Dawuda yă gaishe, yă kuma yi masa barka saboda nasarar da ya yi a kan Hadadezer, gama Hadadezer nan ya hana Towu sakewa. Yoram ya tafi ɗauke da kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla.
11 Os quaes tambem o rei David consagrou ao Senhor, juntamente com a prata e oiro que já havia consagrado de todas as nações que sujeitara,
Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan kayayyaki wa Ubangiji, yadda ya yi da zinariya, da kuma azurfa daga dukan al’umman da ya mallaka,
12 De Syria, e de Moab, e dos filhos d'Ammon, e dos philisteos, e d'Amalek, e dos despojos de Hadadezer, filho de Rechob, rei de Zoba.
wato, azurfa da zinariyan mutanen Edom, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba.
13 Tambem David ganhou nome, voltando elle de ferir os syros no valle do sal, a saber, a dezoito mil.
Dawuda kuwa ya ƙara zama shahararre bayan ya dawo daga kai wa ƙasar Aram hari, daga nan sai ya je ya karkashe mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
14 E poz guarnições em Edom, em todo o Edom poz guarnições, e todos os idumeos ficaram por servos de David: e o Senhor ajudava a David por onde quer que ia.
Ya ajiye rundunar sojoji ko’ina a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba wa Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
15 Reinou pois David sobre todo o Israel: e David fazia direito e justiça a todo o seu povo.
Dawuda ya yi mulkin dukan ƙasar Isra’ila, yana yin wa dukan jama’arsa shari’ar gaskiya da adalci.
16 E Joab, filho de Zeruia, era sobre o exercito; e Josaphat, filho de Ahilud, era chronista.
Yowab ɗan Zeruhiya ya zama shugaban sojoji; Yehoshafat ɗan Ahilud kuwa shi ne marubucin tarihi;
17 E Zadok, filho de Ahitub, e Ahimelek, filho de Abiathar, eram sacerdotes, e Seraias escrivão,
Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyatar, su ne firistoci; Serahiya kuma sakatare;
18 Tambem Benaia, filho de Joiada, estava com os cheretheos e peletheos: porém os filhos de David eram principes.
Benahiya ɗan Yehohiyada ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, wato, sojoji masu gadin Dawuda, sa’an nan’ya’yan Dawuda maza su ne mashawartan sarki.