< 1 Pedro 4 >

1 Ora pois, já que Christo padeceu por nós na carne, armae-vos tambem vós com este pensamento, que aquelle que padeceu na carne já cessou do peccado,
Saboda haka, tunda yake Almasihu ya sha wuya a jiki, muma mu sha damara da wannan ra'ayi. Duk wanda ya sha wuya a jiki ya daina aikata zunubi.
2 Para, no tempo que lhe resta na carne, não viver mais segundo as concupiscencias dos homens, mas segundo a vontade de Deus.
Wannan mutum kuma baya kara zaman biye wa muguwar sha'awar mutumtaka, amma sai dai nufin Allah dukkan sauran kwanakinsa a duniya.
3 Porque basta-nos que no tempo passado da vida obrassemos a vontade dos gentios, andando em dissoluções, concupiscencias, borrachices, glotonerias, bebedices e abominaveis idolatrias,
Gama lokaci ya wuce da zamu yi abin da al'ummai suke son yi, wato fajirci, mugayen sha'awace-sha'awace, da buguwa da shashanci da shaye-shaye da bautar gumaku da abubuwan kyama.
4 O que estranham, por não correrdes com elles no mesmo desenfreamento de dissolução, blasphemando de vós.
Suna tunanin bakon abu ku ke yi da ba kwa hada kai tare da su yanzu a yin wadannan abubuwa, sai suna zarginku.
5 Os quaes hão de dar conta ao que está preparado para julgar os vivos e os mortos.
Za su bada lissafi ga wanda yake a shirye ya shari'anta masu rai da matattu.
6 Porque para isso foi prégado o evangelho tambem aos mortos, para que, na verdade, fossem julgados segundo os homens na carne, porém vivessem segundo Deus em espirito;
Shi yasa aka yi wa matattu wa'azin bishara, cewa ko da shike anyi masu shari'a cikin jikunan mutane, su rayu bisa ga Allah a ruhu.
7 E já está proximo o fim de todas as coisas: portanto sêde sobrios e vigiae em orações.
Karshen dukkan abubuwa yana gabatowa. Saboda haka, ku zama natsatsu, ku natsu cikin tunaninku domin yin addu'oi.
8 Mas, sobretudo, tende ardente caridade uns para com os outros; porque a caridade cobrirá a multidão de peccados.
Gaba da kome, ku himmatu wajen kaunar juna, domin kauna bata neman tona zunuban wadansu.
9 Hospedae-vos uns aos outros, sem murmurações.
Ku yi wa juna bakunta da abubuwa nagari ba tare da gunaguni ba.
10 Cada um administre aos outros o dom como o recebeu, como bons dispenseiros da multiforme graça de Deus.
Yadda kowanne dayanku ya sami baiwa, kuyi amfani da su domin ku kyautata wa juna, kamar masu rikon amanar bayebaye na Allah, wanda ya ba mu hannu sake.
11 Se alguem fallar, falle segundo as palavras de Deus: se alguem administrar, administre segundo o poder que Deus dá; para que em tudo Deus seja glorificado por Jesus Christo, a quem pertence a gloria e poder para todo o sempre. Amen. (aiōn g165)
Idan wani yana yin wa'azi, ya zamana fadar Allah ya ke fadi, idan wani yana hidima, ya yi da karfin da Allah ya ba shi, domin cikin dukkan abubuwa a daukaka Allah ta wurin Yesu Almasihu. Daukaka da iko nasa ne har abada abadin. Amin. (aiōn g165)
12 Amados, não estranheis o ardor que vos sobrevem para vos tentar, como se coisa estranha vos acontecesse;
Ya kaunatattu, kada ku zaci cewa matsananciyar wahalar da ta zo ta gwada ku bakon abu ne, ko kuma wani bakon abu ne yake faruwa a gareku.
13 Mas alegrae-vos de serdes participantes das afflicções de Christo: para que tambem na revelação da sua gloria vos regozijeis e alegreis.
Amma muddin kuna tarayya da Almasihu cikin wahalarsa, ku yi murna, domin kuyi farin ciki da murna sa'adda za a bayyana daukakarsa.
14 Se pelo nome de Christo sois vituperados, bemaventurados sois, porque sobre vós repousa o Espirito da gloria de Deus; o qual, quanto a elles, é blasphemado, mas, quanto a vós, glorificado.
Idan ana zargin ku sabili da sunan Almasihu, ku masu albarka ne, domin Ruhun daukaka da Ruhun Allah ya tabbata a kanku.
15 Porém nenhum de vós padeça como homicida, ou ladrão, ou malfeitor, ou como o que se entremette em negocios alheios;
Amma kada kowannen ku ya sha wahala sabo da horon shi mai kisan kai ne, ko barawo, ko mamugunci, ko mai shisshigi.
16 Mas, se padece como christão, não se envergonhe, antes glorifique a Deus n'esta parte.
Amma in wani yana shan wahala sabili da shi na Almasihu ne, kada ya ji kunya, amma ya daukaka Allah a wannan sunan.
17 Porque já é tempo que comece o juizo pela casa de Deus; e, se primeiro começa por nós, qual será o fim d'aquelles que são desobedientes ao evangelho de Deus?
Domin lokaci ya yi da shari'a za ta fara daga gidan iyalin Allah. Idan kuwa za a fara da mu, menene karshen wadanda suka ki biyayya da bisharar Allah?
18 E, se o justo apenas se salva, onde apparecerá o impio e o peccador?
Idan mutum, “mai adalci ya tsira da kyar, to, me zai faru da marar bin Allah da mai zunubi kuma?”
19 Portanto tambem os que padecem segundo a vontade de Deus encommendem-lhe as suas almas, como ao fiel Creador, fazendo o bem.
Sabo da haka bari wadanda suke shan wuya bisa ga nufin Allah, su mika rayukansu ga amintaccen Mahalicci suna kuma yin ayyuka nagari.

< 1 Pedro 4 >