< 1 Reis 13 >
1 E eis que um homem de Deus veiu de Judah com a palavra do Senhor a Bethel: e Jeroboão estava junto ao altar, para queimar incenso.
Bisa ga umarnin Ubangiji, sai wani mutumin Allah ya zo daga Yahuda zuwa Betel, yayinda Yerobowam yake tsaye kusa da bagade don yă miƙa hadaya.
2 E clamou contra o altar com a palavra do Senhor, e disse: Altar, altar! assim diz o Senhor: Eis que um filho nascerá á casa de David, cujo nome será Josias, o qual sacrificará sobre ti os sacerdotes dos altos que queimam sobre ti incenso, e ossos de homens se queimarão sobre ti.
Sai mutumin Allah ya tā da murya a kan bagade bisa ga umarnin Ubangiji ya ce, “Ya bagade, bagade! Ubangiji ya ce, ‘Za a haifi ɗa mai suna Yosiya wa gidan Dawuda. A kanka zai miƙa firistoci na masujadai kan tuddai masu miƙa hadayu a nan, za a kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kanka.’”
3 E deu n'aquelle mesmo dia um signal, dizendo: Este é o signal de que o Senhor fallou: Eis que o altar se fenderá, e a cinza, que n'elle está, se derramará.
A wannan rana mutumin Allah ya ba da alama, “Ga alamar da Ubangiji ya furta. Wannan bagade zai tsage yă rabu kashi biyu, tokar da yake a kansa za tă zuba a ƙasa.”
4 Succedeu pois, que, ouvindo o rei a palavra do homem de Deus, que clamara contra o altar de Bethel, Jeroboão estendeu a sua mão de sobre o altar, dizendo: Pegae d'elle. Mas a sua mão, que estendera contra elle, se seccou, e não a podia tornar a trazer a si.
Sa’ad da Yerobowam ya ji abin da mutumin Allah ya tā da murya ya faɗa game da bagaden Betel, sai ya miƙa hannunsa daga bagaden ya ce, “Ku kama shi!” Amma sai hannun da ya miƙa ya yanƙwane, har bai iya janye shi ba.
5 E o altar se fendeu, e a cinza se derramou do altar; segundo o signal que o homem de Deus apontara pela palavra do Senhor.
Haka ma, bagaden ya rabu, tokarsa kuma ya zuba, bisa ga alamar da mutumin Allah ya bayar, ta wurin kalmar Ubangiji.
6 Então respondeu o rei, e disse ao homem de Deus: Ora á face do Senhor teu Deus, e roga por mim, que a minha mão se me restitua. Então o homem de Deus orou á face do Senhor, e a mão do rei se lhe restituiu, e ficou como d'antes.
Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Ka roƙi Ubangiji Allahnka, ka kuma yi addu’a domina don hannuna ya warke.” Saboda haka mutumin Allah ya yi roƙo ga Ubangiji, hannun sarki kuwa ya warke, ya kuma zama kamar yadda yake a dā.
7 E o rei disse ao homem de Deus: Vem comigo a casa, e conforta-te; e dar-te-hei um presente.
Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Zo gida tare da ni, ka sami wani abu ka ci, zan kuwa yi maka kyauta.”
8 Porém o homem de Deus disse ao rei: Ainda que me désses metade da tua casa, não iria comtigo, nem comeria pão nem beberia agua n'este logar.
Amma mutumin Allah ya amsa wa sarki, “Ko da za ka ba rabin mallakarka, ba zan tafi tare da kai ba, ba kuwa zan ci abinci, ko in sha ruwa a can ba.
9 Porque assim me ordenou o Senhor pela sua palavra, dizendo: Não comerás pão nem beberás agua; e não voltarás pelo caminho por onde foste
Gama an umarce ni ta wurin kalmar Ubangiji, aka ce, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
10 E foi-se por outro caminho; e não voltou pelo caminho, por onde viera a Bethel.
Saboda haka ya ɗauki wata hanya, bai kuwa koma ta hanyar da ya zo Betel ba.
11 E morava em Bethel um propheta velho; e veiu seu filho, e contou-lhe tudo o que o homem de Deus fizera aquelle dia em Bethel, e as palavras que dissera ao rei; e as contaram a seu pae.
To, fa, akwai wani tsohon annabi yana zama a Betel, wanda’ya’yansa suka zo suka faɗa masa dukan abin da mutumin Allah ya yi a can, a ranar. Suka kuma faɗa wa mahaifinsu abin da ya faɗa wa sarki.
12 E disse-lhes seu pae: Por que caminho se foi? E viram seus filhos o caminho por onde fôra o homem de Deus que viera de Judah.
Mahaifinsu ya tambaye su ya ce, “Wace hanya ce ya bi?” Sai’ya’yansa suka nuna masa hanyar da mutumin Allah daga Yahuda ya bi.
13 Então disse a seus filhos: Albardae-me um jumento. E albardaram-lhe o jumento, e montou n'elle.
Sai ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Da suka yi wa jakin shimfiɗa, sai ya hau.
14 E foi-se apoz o homem de Deus, e o achou assentado debaixo d'um carvalho: e disse-lhe: És tu o homem de Deus que vieste de Judah? E elle disse: Eu sou.
Ya bi bayan mutumin Allah. Ya same shi yana zama a ƙarƙashin itace oak, sai ya tambaye shi ya ce, “Kai ne mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda?” Ya amsa, “Ni ne.”
15 Então lhe disse: Vem comigo a casa, e come pão.
Saboda haka annabin ya ce masa, “Zo gida tare da ni ka ci abinci.”
16 Porém elle disse: Não posso voltar comtigo, nem entrarei comtigo; nem tão pouco comerei pão, nem beberei comtigo agua n'este logar.
Mutumin Allah ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba, ko in ci abinci, ko in sha ruwa tare da kai a can ba.
17 Porque me foi mandado pela palavra do Senhor: Ali nem comerás pão, nem beberás agua; nem tornarás a ir pelo caminho por que foste.
An faɗa mini ta wurin maganar Ubangiji, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa a can, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
18 E elle lhe disse: Tambem eu sou propheta como tu, e um anjo me fallou pela palavra do Senhor, dizendo: Faze-o voltar comtigo a tua casa, para que coma pão e beba agua (Porém mentiu-lhe).
Sai annabin ya amsa, “Ni ma annabi ne, kamar ka. Kuma mala’ika ya ce mini ta wurin kalmar Ubangiji, ‘Dawo da shi zuwa gidanka saboda yă ci abinci, yă kuma sha ruwa.’” (Amma yana masa ƙarya ne.)
19 E tornou elle, e comeu pão em sua casa e bebeu agua.
Sai mutumin Allah ya koma tare da shi ya kuma ci ya sha a gidansa.
20 E succedeu que, estando elles á mesa, a palavra do Senhor veiu ao propheta que o tinha feito voltar.
Yayinda suke zaune a teburi, sai maganar Ubangiji ta zo wa tsohon annabin da ya dawo da mutumin Allah.
21 E clamou ao homem de Deus, que viera de Judah, dizendo: Assim diz o Senhor: Porquanto foste rebelde á bocca do Senhor, e não guardaste o mandamento que o Senhor teu Deus te mandara;
Sai tsohon annabin ya tā da murya wa mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ƙazantar da maganar Ubangiji, ba ka kuma kiyaye umarnin Ubangiji Allahnka ba.
22 Antes voltaste, e comeste pão e bebeste agua no logar de que te dissera: Não comerás pão nem beberás agua; o teu cadaver não entrará no sepulchro de teus paes.
Ka dawo ka ci abinci, ka kuma sha ruwa a wurin da na faɗa maka kada ka ci, ko ka sha. Saboda haka ba za a binne jikinka a kabarin kakanninka ba.’”
23 E succedeu que, depois que comeu pão, e depois que bebeu, albardou elle o jumento para o propheta que fizera voltar.
Sa’ad da mutumin Allah ya gama ci da sha, sai annabin da ya dawo da shi ya yi wa jakin mutumin Allah shimfiɗa.
24 Foi-se pois, e um leão o encontrou no caminho, e o matou: e o seu cadaver estava lançado no caminho, e o jumento estava parado junto a elle, e o leão estava junto ao cadaver.
Yayinda yake kan hanyarsa, sai wani zaki ya sadu da shi ya kashe shi, aka kuma jefar da jikinsa a kan hanya, jakin da zakin suka tsaya kusa da gawar.
25 E eis que os homens passaram, e viram o corpo lançado no caminho, como tambem o leão, que estava junto ao corpo: e vieram, e o disseram na cidade onde o propheta velho habitava.
Waɗansu mutane masu wucewa suka ga an yar da gawar a can, zaki yana tsaye kusa da gawar, sai suka tafi suka ba da labarin a birni inda tsohon annabin nan yake zama.
26 E, ouvindo-o o propheta que o fizera voltar do caminho, disse: É o homem de Deus, que foi rebelde á bocca do Senhor: por isso o Senhor o entregou ao leão, que o despedaçou e matou, segundo a palavra que o Senhor lhe tinha dito.
Sa’ad da annabin da ya dawo da mutumin Allah ya ji, sai ya ce, “Mutumin Allah ne, wanda ya ƙazantar da maganar Ubangiji. Ubangiji ya bashe shi ga zaki, wanda ya yayyage shi ya kuma kashe shi, kamar yadda maganar Ubangiji ta gargaɗe shi.”
27 Então disse a seus filhos: Albardae-me o jumento. Elles o albardaram.
Sai annabin ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Sai suka yi.
28 Então foi, e achou o seu cadaver lançado no caminho, e o jumento e o leão, que estavam parados junto ao cadaver: o leão não tinha devorado o corpo, nem tinha despedaçado o jumento.
Sai ya fita ya sami an jefar da gawar a hanya, jakin da zakin suna tsaye kusa da shi. Zakin bai ci gawar ko yă yayyage jakin ba.
29 Então o propheta levantou o cadaver do homem de Deus, e pôl-o em cima do jumento e o tornou a levar assim veiu o propheta velho á cidade, para o chorar e enterrar.
Saboda haka annabin ya ɗauki gawar mutumin Allah, ya shimfiɗa shi a kan jaki, ya koma da shi cikin birninsa don yă yi makokinsa yă kuma binne shi.
30 E metteu o seu cadaver no seu proprio sepulchro; e prantearam sobre elle, dizendo: Ah irmão meu!
Sai ya kwantar da gawar a kabarinsa, suka yi makoki a kansa, ya kuma ce, “Ayya, abokina!”
31 E succedeu que, depois de o haver sepultado, fallou a seus filhos, dizendo: Morrendo eu, sepultae-me no sepulchro em que o homem de Deus está sepultado: ponde os meus ossos junto aos ossos d'elle.
Bayan an binne shi, sai ya ce wa’ya’yansa, “Sa’ad da na mutu, ku binne ni a kabarin da aka binne mutumin Allah; ku kwantar da ƙasusuwana kusa da ƙasusuwansa.
32 Porque certamente se cumprirá o que pela palavra do Senhor exclamou contra o altar que está em Bethel, como tambem contra todas as casas dos altos que estão nas cidades de Samaria.
Gama annabcin da ya yi ta maganar Ubangiji gāba da bagaden da yake cikin Betel da kuma wuraren sujada a tuddan da suke a biranen Samariya, ba shakka zai cika.”
33 Depois d'estas coisas, Jeroboão não tornou do seu máu caminho; antes dos mais baixos do povo tornou a fazer sacerdotes dos logares altos; a quem queria lhe enchia a mão, e assim era um dos sacerdotes dos logares altos.
Har ma bayan wannan, Yerobowam bai canja daga mugayen hanyoyinsa ba, amma ya ƙara naɗa firistoci domin masujadai da suke kan tuddai daga kowane irin mutane. Duk wanda ya so yă zama firist sai yă naɗa shi don aiki a masujadai da suke kan tuddai.
34 E isso foi causa de peccado á casa de Jeroboão, para destruil-a e extinguil-a da terra.
Wannan ne zunubin gidan Yerobowam da ya kai ga fāɗuwarsa da kuma hallakarsa daga fuskar duniya.