< Rzymian 14 >

1 A tego, kto jest słaby w wierze, przyjmujcie, [lecz] nie po to, aby sprzeczać się [wokół] spornych kwestii.
Ku karɓi wanda bangaskiyarsa ba tă yi ƙarfi ba, amma fa kada ku hukunta shi a kan abubuwan da ake da shakka a kai ba.
2 Jeden bowiem wierzy, że może jeść wszystko, a inny, [będąc] słaby, jada jarzyny.
Bangaskiyar mutum ta yarda masa yă ci kome, amma wanda bangaskiyarsa ba tă yi ƙarfi ba, yakan ci kayan lambu ne kawai.
3 Ten, kto je, niech nie lekceważy tego, który nie je, a ten, kto nie je, niech nie potępia tego, który je, bo Bóg go przyjął.
Mutumin da yake cin kowane irin abinci, kada yă rena wanda ba ya cin, wanda kuma ba ya cin kowane irin abinci, kada yă ga laifin mutumin da yake ci, domin Allah ya riga ya karɓe shi.
4 Kim jesteś ty, że sądzisz cudzego sługę? Dla własnego Pana stoi albo upada. Ostoi się jednak, gdyż Bóg może go utwierdzić.
Kai wane ne har da za ka ga laifin bawan wani? Ko bawan yă yi aiki mai kyau, ko yă kāsa, ai, wannan ruwan maigidansa ne. Za a ma tsai da shi, domin Ubangiji yana da ikon tsai da shi.
5 Jeden bowiem czyni różnicę między dniem a dniem, a drugi każdy dzień ocenia [jednakowo]. Każdy niech będzie dobrze upewniony w swoim zamyśle.
Wani yakan ɗauki wata rana da daraja fiye da sauran ranaku; wani kuma yana ganin dukan ranakun ɗaya ne. Ya kamata kowa yă kasance da tabbaci a cikin zuciyarsa.
6 Kto przestrzega dnia, dla Pana przestrzega, a kto nie przestrzega dnia, dla Pana nie przestrzega. Kto je, dla Pana je, bo dziękuje Bogu, a kto nie je, dla Pana nie je i dziękuje Bogu.
Wannan mai ɗaukan rana ɗaya da muhimmanci fiye da sauran, yana yin haka ne ga Ubangiji. Wannan mai cin nama, yana yin haka ne ga Ubangiji, gama yakan yi godiya ga Allah; wannan da ba ya ci kuwa, yana yin haka ne ga Ubangiji yana kuwa yin godiya ga Allah.
7 Nikt bowiem z nas dla siebie nie żyje i nikt dla siebie nie umiera.
Gama ba waninmu da yake rayuwa wa kansa kaɗai, kuma ba waninmu da kan mutu don kansa kaɗai.
8 Bo jeśli żyjemy, dla Pana żyjemy, jeśli umieramy, dla Pana umieramy. Dlatego czy żyjemy, czy umieramy, należymy do Pana.
In muna rayuwa, muna rayuwa ne ga Ubangiji; in kuma muna mutuwa, muna mutuwa ne ga Ubangiji. Saboda haka, ko muna a raye ko muna a mace, mu na Ubangiji ne.
9 Gdyż po to Chrystus umarł, powstał i ożył, aby panować i [nad] umarłymi, i nad żywymi.
Saboda wannan ne Kiristi ya mutu, ya kuma sāke rayuwa domin yă zama Ubangiji na matattu da na masu rai.
10 Dlaczego więc ty potępiasz swego brata? Albo czemu lekceważysz swego brata? Wszyscy bowiem staniemy przed trybunałem Chrystusa.
Kai kuwa, don me kake ganin laifin ɗan’uwanka? Ko kuma don me kake rena ɗan’uwanka? Gama duk za mu tsaya a gaban kujerar shari’ar Allah.
11 Jest bowiem napisane: Jak żyję, mówi Pan, ugnie się przede mną każde kolano i każdy język będzie wysławiał Boga.
A rubuce yake cewa, “‘Muddin ina raye,’ in ji Ubangiji, ‘kowace gwiwa za tă durƙusa a gabana; kowane harshe kuma zai furta wa Allah.’”
12 Tak więc każdy z nas sam za siebie zda rachunek Bogu.
Don haka kowannenmu zai ba da lissafin kansa ga Allah.
13 A tak już nie osądzajmy jedni drugich, ale raczej uważajcie na to, aby nie dawać bratu powodu do potknięcia się lub upadku.
Saboda haka bari mu daina ba wa juna laifi. A maimakon, sai kowa yă yi niyya ba zai sa dutsen tuntuɓe ko abin sa fāɗuwa a hanyar ɗan’uwansa ba.
14 Wiem i jestem przekonany przez Pana Jezusa, że nie ma niczego, co by samo w sobie było nieczyste. Tylko dla tego, kto uważa coś za nieczyste, [to] dla niego [jest] nieczyste.
A matsayina na mai bin Ubangiji Yesu na tabbata ƙwarai cewa babu abincin da yake marar tsabta don kansa. Amma in wani ya ɗauka wani abu marar tsabta ne, to, a gare shi marar tsabta ne.
15 Lecz jeśli z powodu pokarmu twój brat jest zasmucony, już nie postępujesz zgodnie z miłością. Nie zatracaj swoim pokarmem tego, za którego umarł Chrystus.
In kana ɓata wa ɗan’uwanka zuciya saboda abincin da kake ci, ba halin ƙauna kake nunawa ba ke nan. Kada abincin da kake ci yă zama hanyar lalatar da ɗan’uwanka wanda Kiristi ya mutu dominsa.
16 Niech więc wasze dobro nie będzie bluźnione.
Kada ka bar abin da ka ɗauka a matsayi kyakkyawa yă zama abin zargi ga waɗansu.
17 Królestwo Boże bowiem to nie pokarm i napój, ale sprawiedliwość, pokój i radość w Duchu Świętym.
Gama mulkin Allah ba batun ci da sha ba ne, sai dai na adalci, salama, da kuma farin ciki cikin Ruhu Mai Tsarki,
18 Kto bowiem w tym służy Chrystusowi, podoba się Bogu i cieszy się uznaniem u ludzi.
duk kuwa wanda yake bauta wa Kiristi a haka yana faranta wa Allah rai ne, yardajje kuma ga mutane.
19 Tak więc dążmy do tego, co [służy] pokojowi i wzajemnemu zbudowaniu.
Saboda haka sai mu yi iya ƙoƙari mu aikata abin da zai kawo salama da kuma ingantawa ga juna.
20 Z powodu pokarmu nie niszcz dzieła Bożego. Wszystko wprawdzie jest czyste, ale [staje się] złe dla człowieka, który je ze zgorszeniem.
Kada ku lalatar da aikin Allah saboda abinci. Dukan abinci mai tsabta ne, sai dai ba daidai ba ne mutum yă ci abin da zai sa wani yă yi tuntuɓe.
21 Dobrze jest nie jeść mięsa i nie pić wina ani żadnej [rzeczy], przez którą twój brat się obraża, gorszy albo słabnie.
Ya fi kyau kada ka ci nama ko ka sha ruwan inabi ko kuma ka yi wani abin da zai sa ɗan’uwanka yă fāɗi.
22 Masz wiarę? Miej ją sam u siebie przed Bogiem. Szczęśliwy ten, kto samego siebie nie potępia [w tym], co uważa za dobre.
Bari duk ra’ayin da kake da shi game da wannan sha’ani yă kasance tsakaninka da Allah. Mai albarka ne wanda zuciyarsa ba tă ba shi laifi game da abin da shi da kansa ya ɗauka cewa daidai ne ba.
23 Lecz kto ma wątpliwości, jeśli je, jest potępiony, bo nie je z wiary. Wszystko bowiem, co nie jest z wiary, jest grzechem.
Amma wanda yake da shakka yakan jawo wa kansa hukunci ne in ya ci, domin yana ci ne ba bisa ga bangaskiya ba; kuma duk abin da bai zo daga bangaskiya ba zunubi ne.

< Rzymian 14 >