< Mateusza 13 >
1 A tego dnia Jezus wyszedł z domu i usiadł nad [brzegiem] morza.
A ranan nan sai Yesu ya fita daga gida ya je ya zauna a bakin tafkin.
2 I zebrały się wokół niego wielkie tłumy, dlatego wszedł do łodzi i usiadł, a wszyscy ludzie stali na brzegu.
Taron mutane mai yawan gaske suka taru kewaye da shi har ya kai sai da ya shiga jirgin ruwa ya zauna, yayinda dukan mutane suka tsaya a gaci.
3 I mówił do nich wiele w przypowieściach. I powiedział: Oto siewca wyszedł siać.
Sa’an nan ya faɗa musu abubuwa da yawa cikin misalai, yana cewa, “Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
4 A gdy siał, niektóre [ziarna] padły przy drodze, przyleciały ptaki i wydziobały je.
Da yana yafa irin, waɗansu suka fāffāɗi a kan hanya, tsuntsaye kuwa suka zo suka cinye su.
5 Inne padły na [miejsca] skaliste, gdzie nie miały wiele ziemi. Zaraz wzeszły, bo ziemia nie była głęboka.
Waɗansu suka fāɗi a wurare mai duwatsu, inda babu ƙasa sosai, nan da nan kuwa suka tsira, da yake ƙasar ba zurfi.
6 Lecz gdy wzeszło słońce, zostały spalone, a ponieważ nie miały korzenia, uschły.
Sai dai da rana ta ɗaga, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka kuma yanƙwane domin ba su da saiwa sosai.
7 Inne padły między ciernie, a ciernie wyrosły i zagłuszyły je.
Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya, ƙayan kuwa ta yi girma ta shaƙe su.
8 Inne zaś padły na dobrą ziemię i wydały plon, jedne stokrotny, inne sześćdziesięciokrotny, a jeszcze inne trzydziestokrotny.
Har yanzu, waɗansu irin suka fāffāɗi a ƙasa mai kyau, inda suka ba da amfani riɓi ɗari, sittin ko kuma talatin na abin da aka shuka.
9 Kto ma uszy do słuchania, niech słucha.
Duk mai kunnen ji, yă ji.”
10 Wtedy uczniowie podeszli i zapytali go: Dlaczego mówisz do nich w przypowieściach?
Almajiran suka zo wurinsa suka tambaye shi, “Me ya sa kake wa mutane magana da misalai?”
11 A on odpowiedział im: Wam dano poznać tajemnice królestwa niebieskiego, ale im nie jest dane.
Ya amsa ya ce, “Sanin asirin mulkin sama kam, ku aka ba wa, amma su ba a ba su ba.
12 Kto bowiem ma, temu będzie dodane i będzie miał w obfitości, ale kto nie ma, zostanie mu zabrane nawet to, co ma.
Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, zai kuwa samu a yalwace. Duk wanda kuma ba shi da shi, ko ɗan abin da yake da shi ma, za a karɓe.
13 Dlatego mówię do nich w przypowieściach, bo patrzą, a nie widzą, i słuchają, a nie słyszą ani nie rozumieją.
Abin da ya sa nake musu magana da misalai ke nan. “Ko da yake suna kallo, ba sa gani; ko da yake suna saurara, ba sa ji ko su gane.
14 I spełnia się na nich proroctwo Izajasza, które mówi: Słuchając, będziecie słyszeć, ale nie zrozumiecie i patrząc, będziecie widzieć, ale nie zobaczycie.
A kansu ne aka cika annabcin Ishaya cewa, “‘Za ku yi ta ji amma ba za ku taɓa ganewa ba; za ku yi ta kallo amma ba za ku taɓa gani ba.
15 Utyło bowiem serce tego ludu, stępiały ich uszy i zamknęli swe oczy, żeby przypadkiem oczami nie widzieli ani uszami [nie] słyszeli, a sercem [nie] zrozumieli i [nie] nawrócili się, i żebym ich [nie] uzdrowił.
Gama zuciyar mutanen nan ta taurare; da ƙyar suke ji da kunnuwansu, sun kuma rufe idanunsu. Da ba haka ba, mai yiwuwa su gani da idanunsu, su kuma ji da kunnuwansu, su gane a zuciyarsu, su kuwa juya, in kuma warkar da su.’
16 Ale błogosławione wasze oczy, bo widzą, i wasze uszy, bo słyszą.
Amma idanunku masu albarka ne domin suna gani, haka ma kunnuwanku domin suna ji.
17 Bo zaprawdę powiadam wam: Wielu proroków i sprawiedliwych pragnęło widzieć [to], co [wy] widzicie, ale nie zobaczyli, i słyszeć [to], co [wy] słyszycie, ale nie usłyszeli.
Gama gaskiya nake gaya muku, annabawa da mutane masu adalci da yawa sun yi marmarin ganin abin da kuke gani amma ba su gani ba, su kuma ji abin da kuke ji amma ba su ji ba.
18 Wysłuchajcie więc przypowieści o siewcy.
“To, ku saurari ma’anar misali na mai shukan nan.
19 Gdy ktoś słucha słowa o królestwie, a nie rozumie, przychodzi zły i porywa to, co zostało zasiane w jego sercu. To jest ten posiany przy drodze.
Duk sa’ad da wani ya ji saƙo game da mulkin bai kuwa fahimce shi ba, mugun nan yakan zo yă ƙwace abin da aka shuka a zuciyarsa. Wannan shi ne irin da ya fāɗi a kan hanya.
20 A posiany na [miejscach] skalistych to ten, który słucha słowa i natychmiast z radością je przyjmuje.
Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a wuraren duwatsu kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, nan da nan kuwa yă karɓe ta da murna.
21 Nie ma jednak w sobie korzenia, lecz trwa do czasu. Gdy bowiem przychodzi ucisk albo prześladowanie z powodu słowa, zaraz się gorszy.
Sai dai da yake ba shi da saiwa, yakan ɗan jima kaɗan kawai. Da wata wahala ko tsanani ya auko masa saboda maganar, nan da nan sai yă ja da baya.
22 A posiany między ciernie to ten, który słucha słowa, ale troski tego świata i ułuda bogactwa zagłuszają słowo i staje się [on] bezowocny. (aiōn )
Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi cikin ƙaya kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, sai dai damuwoyin rayuwan nan da jarrabar arzikin duniya sukan shaƙe shi, yă sa maganar ta kāsa amfani. (aiōn )
23 A posiany na dobrej ziemi to ten, który słucha słowa i rozumie je. On też wydaje plon: jeden stokrotny, inny sześćdziesięciokrotny, a jeszcze inny trzydziestokrotny.
Amma wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a ƙasa mai kyau, shi ne mutumin da yakan ji maganar yă kuwa fahimce ta. Yakan ba da amfani wani riɓi ɗari, sittin, ko talatin na abin da aka shuka.”
24 Podał im [też] inną przypowieść: Królestwo niebieskie podobne jest do człowieka, który zasiał dobre ziarno na swoim polu.
Yesu ya ba su wani misali. “Mulkin sama yana kama da wani da ya shuka iri mai kyau a cikin gonarsa.
25 Lecz gdy ludzie spali, przyszedł jego nieprzyjaciel, nasiał kąkolu między pszenicę i odszedł.
Amma yayinda kowa yake barci, abokin gābansa ya zo ya yafa ciyayi a cikin alkamar, ya tafi abinsa.
26 A gdy zboże urosło i wydało plon, wtedy ukazał się też kąkol.
Sa’ad da alkamar ta tashi ta yi kawuna, sai ciyayin ma suka bayyana.
27 Wówczas słudzy gospodarza przyszli i zapytali go: Panie, czy nie posiałeś na swoim polu dobrego ziarna? Skąd więc ten kąkol?
“Bayin mai gonar suka zo wurinsa suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ashe, ba iri mai kyau ka shuka a gonarka ba? To, ina ciyayin nan suka fito?’
28 A on im odpowiedział: Nieprzyjaciel to zrobił. I zapytali go słudzy: Czy chcesz, żebyśmy poszli i zebrali go?
“Sai ya ce, ‘Abokin gāba ne ya yi wannan.’ “Bayin suka tambaye shi suka ce, ‘Kana so mu je mu tuttumɓuke su?’
29 Lecz on odpowiedział: Nie, żebyście przypadkiem, zbierając kąkol, nie wykorzenili razem z nim [i] pszenicy.
“Ya amsa ya ce, ‘A’a, don kada garin tuttumɓuke ciyayi, ku cire har da alkamar.
30 Pozwólcie obydwu razem rosnąć aż do żniwa, a w czasie żniwa powiem żniwiarzom: Zbierzcie najpierw kąkol i zwiążcie go w snopki na spalenie, pszenicę zaś zgromadźcie w moim spichlerzu.
Ku ƙyale su su yi girma tare sai lokacin girbi. A lokacin zan gaya wa masu girbi, da fari ku tara ciyayin ku kuma daure su dami-dami don a ƙone; sa’an nan ku tara alkamar ku kuma kawo su cikin rumbuna.’”
31 Podał im [też] inną przypowieść: Królestwo niebieskie podobne jest do ziarna gorczycy, które człowiek, wziąwszy, zasiał na swoim polu.
Ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da ƙwayar mustad, wadda mutum ya ɗauka ya shuka a gonarsa.
32 Jest ono najmniejsze ze wszystkich nasion, ale kiedy wyrośnie, jest największe ze wszystkich jarzyn i staje się drzewem, tak że ptaki niebieskie przylatują i gnieżdżą się w jego gałęziach.
Ko da yake ita ce mafi ƙanƙanta cikin ƙwayoyinku, duk da haka sa’ad da ta yi girma, takan zama mafi girma cikin tsire-tsiren lambu ta kuma zama itace, har tsuntsayen sararin sama su zo su yi sheƙa a rassansa.”
33 Opowiedział im [jeszcze] inną przypowieść: Królestwo niebieskie podobne jest do zakwasu, który kobieta wzięła i włożyła w trzy miary mąki, aż wszystko się zakwasiło.
Har yanzu ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da yisti wanda mace ta ɗauka ta kwaɓa garin alkama mai yawa, har sai da yistin ya gauraye yistin duka.”
34 To wszystko mówił Jezus do tłumu w przypowieściach, a bez przypowieści nic do nich nie mówił;
Yesu ya faɗa wa taron dukan waɗannan abubuwa cikin misalai; bai faɗa musu kome ba, sai tare da yin amfani da misalai.
35 Aby się wypełniło, co zostało powiedziane przez proroka: Otworzę moje usta w przypowieściach, wypowiem rzeczy ukryte od założenia świata.
Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta wurin annabi cewa, “Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi abubuwan da suke ɓoye tun halittar duniya.”
36 Wtedy Jezus odprawił tłum i przyszedł do domu. Podeszli do niego jego uczniowie i mówili: Wyjaśnij nam przypowieść o kąkolu na polu.
Sa’an nan ya bar taron ya shiga gida. Almajiransa kuwa suka zo wurinsa suka ce, “Bayyana mana misalin ciyayin nan a gona.”
37 A on odpowiedział im: Tym, który sieje dobre ziarno, jest Syn Człowieczy.
Ya amsa ya ce, “Mai yafa irin mai kyan nan, shi ne Ɗan Mutum.
38 Polem jest świat, dobrym ziarnem są synowie królestwa, kąkolem zaś są synowie złego.
Gonar kuwa ita ce duniya, irin nan mai kyau kuwa suna a matsayin’ya’yan mulkin. Ciyayin nan kuma su ne’ya’yan mugun nan,
39 Nieprzyjacielem, który go posiał, jest diabeł, żniwem jest koniec świata, a żniwiarzami są aniołowie. (aiōn )
abokin gāban da yake shuka su kuwa, Iblis ne. Lokacin girbi kuma shi ne ƙarshen zamani, masu girbin kuwa su ne mala’iku. (aiōn )
40 Jak więc zbiera się kąkol i spala w ogniu, tak będzie przy końcu tego świata. (aiōn )
“Kamar yadda aka tattara ciyayin aka kuma ƙone a wuta, haka zai zama a ƙarshen zamani. (aiōn )
41 Syn Człowieczy pośle swoich aniołów, a oni zbiorą z jego królestwa wszystkie zgorszenia i tych, którzy popełniają nieprawość;
Ɗan Mutum zai aiki mala’ikunsa, su kuwa cire daga mulkinsa kome da yake jawo zunubi da kuma duk masu aikata mugunta.
42 I wrzucą ich do pieca ognistego. Tam będzie płacz i zgrzytanie zębów.
Za su jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
43 Wtedy sprawiedliwi będą jaśnieć jak słońce w królestwie swego Ojca. Kto ma uszy do słuchania, niech słucha.
Sa’an nan masu adalci za su haskaka kamar rana a mulkin Ubansu. Duk mai kunnen ji, yă ji.”
44 Ponownie królestwo niebieskie jest podobne do skarbu ukrytego w polu, który człowiek znalazł i ukrył. Uradowany nim poszedł, sprzedał wszystko, co miał, i kupił to pole.
“Mulkin sama yana kama da dukiyar da aka ɓoye a gona. Da wani ya same ta, sai yă sāke ɓoye ta, sa’an nan cikin farin cikinsa yă je yă sayar da duk abin da yake da shi yă sayi gonar.
45 Królestwo niebieskie podobne jest też do kupca, który szukał pięknych pereł.
“Har wa yau dai, mulkin sama yana kama da ɗan kasuwa mai neman lu’ulu’ai masu kyau.
46 A znalazłszy jedną bardzo cenną perłę, poszedł, sprzedał wszystko, co miał, i kupił ją.
Da ya sami dutse guda mai daraja sosai, sai ya tafi ya sayar da dukan abin da yake da shi ya saye shi.
47 Królestwo niebieskie podobne jest również do sieci zarzuconej w morze i zagarniającej [ryby] wszelkiego rodzaju.
“Har yanzu, mulkin sama yana kama da abin kamun kifin da aka jefa cikin tafki yă kamo kifi iri-iri.
48 Gdy się napełniła, [rybacy] wyciągnęli ją na brzeg, a usiadłszy, dobre [ryby] wybrali do naczyń, a złe wyrzucili.
Da abin kamun kifi ya cika, masuntan suka jawo shi gaci. Sai suka zauna suka tattara kifi masu kyau a kwanduna, amma suka zubar da marasa kyau.
49 Tak będzie przy końcu świata: wyjdą aniołowie i wyłączą złych spośród sprawiedliwych; (aiōn )
Haka zai kasance a ƙarshen zamani. Mala’iku za su zo su ware masu mugunta daga masu adalci (aiōn )
50 I wrzucą ich do pieca ognistego. Tam będzie płacz i zgrzytanie zębów.
su kuma jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”
51 Jezus ich zapytał: Zrozumieliście to wszystko? Odpowiedzieli mu: Tak, Panie.
Yesu ya tambaye su ya ce, “Kun gane dukan waɗannan abubuwa?” Suka amsa, “I.”
52 A on powiedział do nich: Dlatego każdy uczony w Piśmie, [który jest] pouczony o królestwie niebieskim, podobny jest do gospodarza, który wydobywa ze swego skarbca nowe i stare rzeczy.
Sa’an nan ya ce musu, “Saboda haka duk malamin dokokin da ya horu game da koyarwar mulkin sama, yana kama da maigida wanda yakan fitar daga ɗakin ajiyarsa sababbin dukiya da kuma tsofaffi.”
53 Kiedy Jezus dokończył tych przypowieści, odszedł stamtąd.
Sa’ad da Yesu ya gama ba da waɗannan misalai, sai ya ci gaba daga can.
54 A przyszedłszy w swoje rodzinne strony, nauczał ludzi w ich synagodze, tak że się bardzo zdumiewali i mówili: Skąd on ma tę mądrość i moc?
Yana isowa garinsa, sai ya fara koya wa mutane a cikin majami’arsu, suka kuwa yi mamaki. Suka yi ta tambaya suna cewa, “Ina wannan mutum ya sami irin wannan hikima da kuma ayyukan banmamaki haka?
55 Czyż to nie jest syn cieśli? Czyż jego matce nie jest na imię Maria, a jego bracia [to] Jakub, Józef, Szymon i Juda?
Wannan ba shi ne ɗan kafinta nan ba? Ba mahaifiyarsa ba ce Maryamu,’yan’uwansa kuma Yaƙub, Yusuf, Siman da Yahuda ba?
56 A jego siostry, czyż wszystkie nie są wśród nas? Skąd więc on ma to wszystko?
Duk’yan’uwansa mata kuma ba tare da mu suke ba? To, a ina wannan mutum ya sami dukan waɗannan abubuwa?”
57 I byli nim zgorszeni. Lecz Jezus powiedział do nich: Nigdzie nie jest prorok bez czci, tylko w swojej ojczyźnie i w swoim domu.
Sai suka ji haushinsa. Amma Yesu ya ce musu, “Sai a garinsa da kuma a gidansa na kaɗai annabi ba ya samun girma.”
58 I nie uczynił tam wielu cudów z powodu ich niewiary.
Bai kuwa yi abubuwan banmamaki da yawa a can ba saboda rashin bangaskiyarsu.