< Mateusza 1 >

1 Księga rodu Jezusa Chrystusa, syna Dawida, syna Abrahama.
Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.
2 Abraham spłodził Izaaka, a Izaak spłodził Jakuba, a Jakub spłodził Judę i jego braci.
Ibrahim ya haifi Ishaku, Ishaku ya haifi Yaƙub, Yaƙub ya haifi Yahuda da’yan’uwansa,
3 A Juda spłodził z Tamar Faresa i Zarę, a Fares spłodził Ezroma, a Ezrom spłodził Arama.
Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu; Ferez ya haifi Hezron, Hezron ya haifi Ram,
4 A Aram spłodził Aminadaba, a Aminadab spłodził Naasona, a Naason spłodził Salmona.
Ram ya haifi Amminadab, Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
5 A Salmon spłodził z Rachab Booza, a Booz spłodził z Rut Obeda, a Obed spłodził Jessego.
Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa, Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa, Obed ya haifi Yesse,
6 A Jesse spłodził króla Dawida, a król Dawid spłodził Salomona z tej, która [była żoną] Uriasza.
Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda. Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.
7 A Salomon spłodził Roboama, a Roboam spłodził Abiasza, a Abiasz spłodził Azę.
Solomon ya haifi Rehobowam, Rehobowam ya haifi Abiya, Abiya ya haifi Asa,
8 A Aza spłodził Jozafata, a Jozafat spłodził Jorama, a Joram spłodził Ozjasza.
Asa ya haifi Yehoshafat, Yehoshafat ya haifi Yehoram, Yehoram ya haifi Azariya,
9 A Ozjasz spłodził Joatama, a Joatam spłodził Achaza, a Achaz spłodził Ezechiasza.
Azariya ya haifi Yotam, Yotam ya haifi Ahaz, Ahaz ya haifi Hezekiya,
10 A Ezechiasz spłodził Manassesa, a Manasses spłodził Amona, a Amon spłodził Jozjasza.
Hezekiya ya haifi Manasse, Manasse ya haifi Amon, Amon ya haifi Yosiya,
11 A Jozjasz spłodził Jechoniasza i jego braci w czasie uprowadzenia do Babilonu.
Yosiya kuma ya haifi Yekoniya da’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.
12 A po uprowadzeniu do Babilonu Jechoniasz spłodził Salatiela, a Salatiel spłodził Zorobabela.
Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon. Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel, Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,
13 A Zorobabel spłodził Abiuda, a Abiud spłodził Eliakima, a Eliakim spłodził Azora.
Zerubbabel ya haifi Abiyud, Abiyud ya haifi Eliyakim, Eliyakim ya haifi Azor,
14 A Azor spłodził Sadoka, a Sadok spłodził Achima, a Achim spłodził Eliuda.
Azor ya haifi Zadok, Zadok ya haifi Akim, Akim kuma ya haifi Eliyud,
15 A Eliud spłodził Eleazara, a Eleazar spłodził Matana, a Matan spłodził Jakuba.
Eliyud ya haifi Eleyazar, Eleyazar ya haifi Mattan, Mattan ya haifi Yaƙub,
16 A Jakub spłodził Józefa, męża Marii, z której narodził się Jezus, zwany Chrystusem.
Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.
17 Tak więc wszystkich pokoleń od Abrahama aż do Dawida [jest] czternaście; a od Dawida aż do uprowadzenia do Babilonu – pokoleń czternaście; a od uprowadzenia do Babilonu aż do Chrystusa – pokoleń czternaście.
Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.
18 A z narodzeniem Jezusa Chrystusa było tak: Gdy Maria, jego matka, została zaślubiona Józefowi, zanim się zeszli, okazało się, że jest brzemienna z Ducha Świętego.
Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
19 Ale Józef, jej mąż, będąc sprawiedliwym i nie chcąc jej zniesławić, chciał ją potajemnie oddalić.
Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.
20 A gdy o tym rozmyślał, oto anioł Pana ukazał mu się we śnie i powiedział: Józefie, synu Dawida, nie bój się przyjąć Marii, twojej żony. To bowiem, co się w niej poczęło, jest z Ducha Świętego.
Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne.
21 I urodzi syna, któremu nadasz imię Jezus. On bowiem zbawi swój lud od jego grzechów.
Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”
22 A to wszystko się stało, aby się wypełniło, co powiedział Pan przez proroka:
Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa,
23 Oto dziewica będzie brzemienna i urodzi syna, któremu nadadzą imię Emmanuel, co się tłumaczy: Bóg z nami.
“Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel” (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).
24 Wtedy Józef, obudziwszy się ze snu, uczynił tak, jak mu rozkazał anioł Pana, i przyjął swoją żonę.
Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa.
25 Ale nie obcował z nią, dopóki nie urodziła swego pierworodnego syna, któremu nadał imię Jezus.
Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.

< Mateusza 1 >