< I Jana 3 >
1 Patrzcie, jaką miłością obdarzył nas Ojciec, że zostaliśmy nazwani dziećmi Bożymi. Dlatego świat nas nie zna, bo jego nie zna.
Dubi irin ƙaunar da Uba ya ƙaunace mu da ita mana, har ana ce da mu’ya’yan Allah! Haka kuwa muke! Dalilin da ya sa duniya ba tă san mu ba shi ne, don ba tă san shi ba.
2 Umiłowani, teraz jesteśmy dziećmi Bożymi, ale jeszcze się nie objawiło, czym będziemy. Wiemy jednak, że gdy [on] się objawi, będziemy podobni do niego, gdyż ujrzymy go takim, jakim jest.
Abokaina ƙaunatattu, yanzu, mu’ya’yan Allah ne, kuma abin da za mu zama nan gaba ba a riga an bayyana ba. Sai dai mun san cewa sa’ad da Kiristi ya bayyana, za mu zama kamar sa, domin za mu gan shi kamar yadda yake.
3 A każdy, kto pokłada w nim tę nadzieję, oczyszcza się, jak i on jest czysty.
Duk mai wannan bege a cikinsa yakan tsarkake kansa, kamar yadda shi Kiristi yake da tsabta.
4 Każdy, kto popełnia grzech, przekracza też prawo, ponieważ grzech jest przekroczeniem prawa.
Duk mai yin zunubi yana karya doka ne; tabbatacce, zunubi, karya doka ne.
5 A wiecie, że on się objawił, aby zgładzić nasze grzechy, a w nim nie ma grzechu.
Sai dai kun san cewa Kiristi ya bayyana ne domin yă ɗauke zunubanmu. A cikinsa kuwa babu zunubi.
6 Każdy [więc], kto w nim trwa, nie grzeszy. Każdy, kto grzeszy, nie widział go ani go nie poznał.
Ba mai rayuwa a cikinsa da yake cin gaba da yin zunubi. Kowa da yake aikata zunubi, bai taɓa ganinsa ba, bai ma san shi ba.
7 Dzieci, niech was nikt nie zwodzi. Kto czyni sprawiedliwość, jest sprawiedliwy, tak jak [i] on jest sprawiedliwy.
’Ya’yana ƙaunatattu, kada ku yarda wani yă ruɗe ku. Duk mai yin abin da yake daidai mai adalci ne, yadda Kiristi yake mai adalci.
8 Kto popełnia grzech, jest z diabła, gdyż diabeł od początku grzeszy. Po to objawił się Syn Boży, aby zniszczyć dzieła diabła.
Duk mai aikata abin da yake zunubi shi na Iblis ne, domin Iblis mai aikata zunubi ne tun farko. Dalilin da ya sa Ɗan Allah ya bayyana kuwa shi ne don yă rushe aikin Iblis.
9 Każdy, kto się narodził z Boga, nie popełnia grzechu, bo jego nasienie w nim pozostaje i nie może grzeszyć, gdyż narodził się z Boga.
Babu haifaffe na Allah da zai ci gaba da yin zunubi, domin iri na Allah yana a cikinsa; ba zai iya ci gaba da yin zunubi ba, domin haifaffe ne na Allah.
10 Po tym poznaje się dzieci Boże i dzieci diabła: Każdy, kto nie czyni sprawiedliwości, nie jest z Boga, [jak] i ten, kto nie miłuje swego brata.
Ta haka muka san waɗanda suke’ya’yan Allah da kuma waɗanda suke’ya’yan Iblis. Duk wanda ba ya yin abin da yake daidai, ba ɗan Allah ba ne; haka ma wanda ba ya ƙaunar ɗan’uwansa.
11 To jest przesłanie, które słyszeliście od początku, że mamy się wzajemnie miłować.
Wannan shi ne saƙon da kuka ji tun farko. Ya kamata mu ƙaunaci juna.
12 Nie jak Kain, [który] pochodził od złego i zabił swego brata. A dlaczego go zabił? Bo jego uczynki były złe, a jego brata sprawiedliwe.
Kada ku zama kamar Kayinu, wanda ya zama na mugun nan, ya kuma kashe ɗan’uwansa. Me ya sa ya kashe shi? Domin ayyukansa mugaye ne, na ɗan’uwansa kuma na adalci ne.
13 Nie dziwcie się, moi bracia, jeśli świat was nienawidzi.
Kada ku yi mamaki’yan’uwana, in duniya ta ƙi ku.
14 My wiemy, że przeszliśmy ze śmierci do życia, bo miłujemy braci. Kto nie miłuje brata, pozostaje w śmierci.
Mun san cewa mun riga mun ratsa daga mutuwa zuwa rai, domin muna ƙaunar’yan’uwanmu. Duk wanda ba ya ƙauna matacce ne har yanzu.
15 Każdy, kto nienawidzi swego brata, jest mordercą, a wiecie, że żaden morderca nie ma życia wiecznego zostającego w sobie. (aiōnios )
Duk mai ƙin ɗan’uwansa mai kisankai ne, kun kuma san cewa ba mai kisankan da yake da rai madawwami a cikinsa. (aiōnios )
16 Po tym poznaliśmy miłość [Boga], że on oddał za nas swoje życie. My również powinniśmy oddawać życie za braci.
Yadda muka san ƙauna ke nan, wato, Yesu Kiristi ya ba da ransa dominmu. Ya kamata mu ma mu ba da rayukanmu domin’yan’uwanmu.
17 A kto miałby majętność tego świata i widziałby swego brata w potrzebie, a zamknąłby przed nim swoje serce, jakże może mieszkać w nim miłość Boga?
In wani yana da arziki, ya kuma ga ɗan’uwansa cikin rashi, bai kuwa taimake shi ba, anya, ƙaunar Allah tana a cikinsa kuwa?
18 Moje dzieci, nie miłujmy słowem ani językiem, ale uczynkiem i prawdą.
’Ya’yana ƙaunatattu, kada mu yi ƙauna da fatar baki kawai, sai dai mu nuna ta ta wurin aikatawa da kuma gaskiya.
19 Po tym poznamy, że jesteśmy z prawdy i uspokoimy przed nim nasze serca.
Ta haka muka san cewa mu na gaskiya ne, kuma za mu iya tsaya a gaban Allah ba tare da rawar jiki ba.
20 Bo jeśli nasze serce nas potępia, Bóg jest większy niż nasze serce i wie wszystko.
Idan zuciyarmu ta nuna mana muna da laifi, mun san cewa Allah ya fi zuciyarmu, ya kuma san dukan kome.
21 Umiłowani, jeśli nasze serce nas nie potępia, mamy ufność ku Bogu;
Abokaina ƙaunatattu, in zukatanmu ba su ba mu laifi ba, muna da ƙarfin halin tsayawa a gaban Allah ke nan.
22 I o cokolwiek prosimy, otrzymujemy od niego, bo zachowujemy jego przykazania i robimy to, co miłe w jego oczach.
Muna kuma samun dukan abin da muka roƙa daga gare shi, domin muna biyayya da umarnansa, muna kuma yin abin da ya gamshe shi.
23 A to jest jego przykazanie, abyśmy wierzyli w imię jego Syna, Jezusa Chrystusa, i miłowali się wzajemnie, jak nam przykazał.
Umarninsa kuwa shi ne, mu gaskata da sunan Ɗansa, Yesu Kiristi, mu kuma ƙaunaci juna kamar yadda ya umarce mu.
24 Bo kto zachowuje jego przykazania, mieszka w nim, a on w nim. A wiemy, że w nas mieszka, przez Ducha, którego nam dał.
Waɗanda suke biyayya da umarnansa kuwa suna rayuwa a cikinsa, shi kuma a cikinsu. Ta haka muka san cewa yana raye a cikinmu. Mun san haka ta wurin Ruhun da ya ba mu.