< Mateusza 7 >
1 Nie sądźcie, abyście nie byli sądzeni;
“Kada ku ba wa kowa laifi, don kada a ba ku laifi ku ma.
2 Albowiem jakim sądem sądzicie, takim sądzeni będziecie, i jaką miarą mierzycie, taką wam odmierzono będzie.
Gama da irin shari’ar da kuka yi wa waɗansu, da ita za a shari’anta ku. Mudun da kuka yi awo da shi, da shi za a yi muku.
3 A czemuż widzisz źdźbło w oku brata twego, a balki, która jest w oku twojem, nie baczysz?
“Don me kake duban ɗan tsinken da yake idon ɗan’uwanka, alhali kuwa ga gungume a naka ido?
4 Albo jakoż rzeczesz bratu twemu: Dopuść, iż wyjmę źdźbło z oka twego, a oto balka jest w oku twojem.
Yaya za ka ce wa ɗan’uwanka, ‘Bari in cire maka ɗan tsinken nan daga idonka,’ alhali kuwa a kowane lokaci akwai gungume a naka ido?
5 Obłudniku! wyjmij pierwej balkę z oka twego, tedy przejrzysz, abyś wyjął źdźbło z oka brata twego.
Kai munafuki, fara cire gungumen da yake idonka, a sa’an nan ne za ka iya gani sosai yadda za ka cire ɗan tsinken da yake a idon ɗan’uwanka.
6 Nie dawajcie świętego psom, ani miećcie pereł waszych przed świnie, by ich snać nie podeptały nogami swemi, i obróciwszy się nie rozszarpały was.
“Kada ku ba karnuka abin da yake mai tsarki; kada kuma ku jefa wa aladu lu’ulu’anku. In kuka yi haka za su tattake su, sa’an nan su juyo su jijji muku ciwo.
7 Proście, a będzie wam dano, szukajcie, a znajdziecie; kołaczcie, a będzie wam otworzono.
“Ku roƙa za a ba ku; ku nema za ku samu; ku ƙwanƙwasa za a kuwa buɗe muku ƙofa.
8 Każdy bowiem, kto prosi, bierze; a kto szuka, znajduje; a temu, co kołacze, będzie otworzono.
Gama duk wanda ya roƙa, akan ba shi; wanda ya nema kuwa, yakan samu, wanda kuma ya ƙwanƙwasa, za a buɗe masa ƙofa.
9 I któryż z was jest człowiek, którego prosiłliby syn jego o chleb, izali mu da kamień?
“Wane ne a cikinku in ɗansa ya roƙe shi burodi, sai yă ba shi dutse?
10 A prosiłby o rybę, izali mu da węża?
Ko kuwa in ya roƙe shi kifi, sai yă ba shi maciji?
11 Jeźli wy tedy będąc złymi, umiecie dary dobre dawać dzieciom waszym, czemże więcej Ojciec wasz, który jest w niebiesiech, da rzeczy dobre tym, którzy go proszą.
In ku da kuke mugaye kun san yadda za ku ba da kyautai masu kyau ga’ya’yanku, balle Ubanku na sama, ba zai fi ku iya ba da abubuwa masu kyau, ga su waɗanda suka roƙe shi ba!
12 Wszystko tedy, co byście chcieli, aby wam ludzie czynili, tak i wy czyńcie im; tenci bowiem jest zakon i prorocy.
Saboda haka, duk abin da kuke so mutane su yi muku, ku ma sai ku yi musu, domin wannan shi ne Doka da koyarwar Annabawa sun ƙunsa.
13 Wchodźcie przez ciasną bramę; albowiem przestronna jest brama i szeroka droga, która prowadzi na zatracenie, a wiele ich jest, którzy przez nię wchodzą.
“Ku shiga ta matsattsiyar ƙofa. Gama ƙofar zuwa hallaka faɗaɗɗiya ce mai sauƙin bi kuma, masu shiga ta cikinta kuwa suna da yawa.
14 A ciasna jest brama i wąska droga, która prowadzi do żywota; a mało ich jest, którzy ją znajdują.
Amma ƙofar zuwa rai, ƙarama ce matsattsiya kuma, masu samunta kuwa kaɗan ne.
15 A strzeżcie się fałszywych proroków, którzy przychodzą do was w odzieniu owczem, ale wewnątrz są wilcy drapieżni.
“Ku yi hankali da annabawan ƙarya. Sukan zo muku da kamannin tumaki, amma daga ciki mugayen kyarketai ne.
16 Z owoców ich poznacie je; izali zbierają z ciernia grona winne, albo z ostu figi?
Ta wurin aikinsu za ku gane su. Mutane suna iya tsinkan inabi a jikin ƙaya, ko kuwa ɓaure a jikin sarƙaƙƙiya?
17 Tak ci wszelkie drzewo dobre owoce dobre przynosi; ale złe drzewo owoce złe przynosi.
Haka ma kowane itace mai kyau yakan ba da’ya’ya masu kyau, kuma mummunan itace ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
18 Nie może dobre drzewo owoców złych przynosić, ani drzewo złe owoców dobrych przynosić.
Itace mai kyau ba ya ba da munanan’ya’ya, haka kuma mummunan itace ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
19 Wszelkie drzewo, które nie przynosi owocu dobrego, bywa wycięte i w ogień wrzucone.
Duk itacen da ba ya ba da’ya’ya masu kyau sai a sare shi a jefa cikin wuta.
20 A tak z owoców ich poznacie je.
Ta haka, ta wurin aikinsu za ku gane su.”
21 Nie każdy, który mi mówi: Panie, Panie! wnijdzie do królestwa niebieskiego; ale który czyni wolę Ojca mojego, który jest w niebiesiech.
“Ba duk mai ce mini, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ ne zai shiga mulkin sama ba, sai dai wanda yake aikata nufin Ubana da yake sama.
22 Wiele ich rzecze mi dnia onego: Panie, Panie! izażeśmy w imieniu twojem nie prorokowali, i w imieniu twojem dyjabłów nie wyganiali, i w imieniu twojem wiele cudów nie czynili?
Da yawa za su ce mini a wannan rana, ‘Ubangiji, Ubangiji, ashe, ba mu yi annabci a cikin sunanka ba, ba kuma a cikin sunanka ne muka fitar da aljanu, muka yi abubuwan banmamaki da yawa ba?’
23 A tedy im wyznam: Żem was nigdy nie znał; odstąpcie ode mnie, którzy czynicie nieprawość.
Sa’an nan zan ce musu a fili, ‘Ban taɓa saninku ba. Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta!’
24 Wszelkiego tedy, który słucha tych słów moich i czyni je, przypodobam mężowi mądremu, który zbudował dom swój na opoce;
“Saboda haka duk wanda yake jin kalmomin nan nawa yake kuma aikata su, yana kama da mutum mai hikima wanda ya gina gidansa a kan dutse.
25 I spadł gwałtowny deszcz, i przyszła powódź, i wiatry wiały, i uderzyły na on dom, ale nie upadł, bo był założony na opoce.
Ruwan sama ya sauko, rafuffuka suka cika, iska kuma ta hura ta bugi gidan; duk da haka bai fāɗi ba, gama yana da harsashinsa a kan dutse.
26 A wszelki, który słucha tych słów moich, a nie czyni ich, przypodobany będzie mężowi głupiemu, który zbudował dom swój na piasku;
Amma duk wanda yake jin kalmomin nan nawa bai kuwa aikata su ba, yana kama da wani wawa wanda ya gina gidansa a kan yashi.
27 I spadł deszcz gwałtowny, i przyszła powódź, i wiatry wiały, a uderzyły na on dom, i upadł, a był wielki upadek jego.
Ruwan sama ya sauko, rafuffuka suka cika, iska kuwa ta hura ta bugi gidan, sai ya fāɗi da mummunar ragargajewa kuwa.”
28 I stało się, gdy dokończył Jezus tych słów, że się zdumiewał lud nad nauką jego.
Sa’ad da Yesu ya gama faɗin waɗannan abubuwa, sai taron mutanen suka yi mamakin koyarwarsa,
29 Albowiem je uczył jako moc mający, a nie jako nauczeni w Piśmie.
domin ya koyar kamar wani wanda yake da iko, ba kamar malamansu na dokoki ba.