< Mateusza 13 >
1 A dnia onego wyszedłszy Jezus z domu, usiadł nad morzem:
A ranan nan sai Yesu ya fita daga gida ya je ya zauna a bakin tafkin.
2 I zebrał się do niego wielki lud, tak iż wstąpiwszy w łódź, siedział, a wszystek lud stał na brzegu.
Taron mutane mai yawan gaske suka taru kewaye da shi har ya kai sai da ya shiga jirgin ruwa ya zauna, yayinda dukan mutane suka tsaya a gaci.
3 I mówił do nich wiele w podobieństwach i rzekł: Oto wyszedł rozsiewca, aby rozsiewał;
Sa’an nan ya faɗa musu abubuwa da yawa cikin misalai, yana cewa, “Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
4 A gdy on rozsiewał, niektóre padło podle drogi; i przyleciały ptaki, a podziobały je.
Da yana yafa irin, waɗansu suka fāffāɗi a kan hanya, tsuntsaye kuwa suka zo suka cinye su.
5 Drugie zasię padło na miejsce opoczyste, gdzie nie miało wiele ziemi; i wnet weszło, iż nie miało głębokości ziemi.
Waɗansu suka fāɗi a wurare mai duwatsu, inda babu ƙasa sosai, nan da nan kuwa suka tsira, da yake ƙasar ba zurfi.
6 Ale gdy słońce weszło, wygorzało, a iż nie miało korzenia, uschło.
Sai dai da rana ta ɗaga, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka kuma yanƙwane domin ba su da saiwa sosai.
7 A drugie padło między ciernie, i wzrosły ciernie, a zadusiły je.
Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya, ƙayan kuwa ta yi girma ta shaƙe su.
8 A drugie padło na ziemię dobrą i wydało pożytek, jedno setny, drugie sześćdziesiątny, a drugie trzydziestny.
Har yanzu, waɗansu irin suka fāffāɗi a ƙasa mai kyau, inda suka ba da amfani riɓi ɗari, sittin ko kuma talatin na abin da aka shuka.
9 Kto ma uszy ku słuchaniu, niechaj słucha.
Duk mai kunnen ji, yă ji.”
10 Tedy przystąpiwszy uczniowie, rzekli mu: Dlaczegoż im w podobieństwach mówisz?
Almajiran suka zo wurinsa suka tambaye shi, “Me ya sa kake wa mutane magana da misalai?”
11 A on odpowiadając, rzekł im: Wam dano wiedzieć tajemnicę królestwa niebieskiego, ale onym nie dano;
Ya amsa ya ce, “Sanin asirin mulkin sama kam, ku aka ba wa, amma su ba a ba su ba.
12 Albowiem kto ma, będzie mu dano, i obfitować będzie, ale kto nie ma, i to, co ma, będzie od niego odjęto.
Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, zai kuwa samu a yalwace. Duk wanda kuma ba shi da shi, ko ɗan abin da yake da shi ma, za a karɓe.
13 Dlategoć im w podobieństwach mówię, iż widząc nie widzą, i słysząc nie słyszą, ani rozumieją.
Abin da ya sa nake musu magana da misalai ke nan. “Ko da yake suna kallo, ba sa gani; ko da yake suna saurara, ba sa ji ko su gane.
14 I pełni się w nich proroctwo Izajaszowe, które mówi: Słuchem słuchać będziecie, ale nie zrozumiecie; i widząc widzieć będziecie, ale nie ujrzycie;
A kansu ne aka cika annabcin Ishaya cewa, “‘Za ku yi ta ji amma ba za ku taɓa ganewa ba; za ku yi ta kallo amma ba za ku taɓa gani ba.
15 Albowiem zatyło serce ludu tego, a uszyma ciężko słyszeli, i oczy swe zamrużyli, żeby kiedy oczyma nie widzieli i uszyma nie słyszeli, a sercem nie zrozumieli, i nie nawrócili się, a uzdrowiłbym je.
Gama zuciyar mutanen nan ta taurare; da ƙyar suke ji da kunnuwansu, sun kuma rufe idanunsu. Da ba haka ba, mai yiwuwa su gani da idanunsu, su kuma ji da kunnuwansu, su gane a zuciyarsu, su kuwa juya, in kuma warkar da su.’
16 Ale oczy wasze błogosławione, że widzą, i uszy wasze, że słyszą;
Amma idanunku masu albarka ne domin suna gani, haka ma kunnuwanku domin suna ji.
17 Bo zaprawdę powiadam wam, iż wiele proroków i sprawiedliwych żądało widzieć to, co wy widzicie, ale nie widzieli, i słyszeć to, co słyszycie, ale nie słyszeli.
Gama gaskiya nake gaya muku, annabawa da mutane masu adalci da yawa sun yi marmarin ganin abin da kuke gani amma ba su gani ba, su kuma ji abin da kuke ji amma ba su ji ba.
18 Wy tedy słuchajcie podobieństwa onego rozsiewcy.
“To, ku saurari ma’anar misali na mai shukan nan.
19 Gdy kto słucha słowa o tem królestwie, a nie rozumie, przychodzi on zły i porywa to, co wsiano w serce jego; tenci jest on, który podle drogi posiany jest.
Duk sa’ad da wani ya ji saƙo game da mulkin bai kuwa fahimce shi ba, mugun nan yakan zo yă ƙwace abin da aka shuka a zuciyarsa. Wannan shi ne irin da ya fāɗi a kan hanya.
20 A na opoczystych miejscach posiany, ten jest, który słucha słowa i zaraz je z radością przyjmuje;
Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a wuraren duwatsu kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, nan da nan kuwa yă karɓe ta da murna.
21 Ale nie ma korzenia w sobie, lecz doczesny jest; a gdy przychodzi ucisk, albo prześladowanie dla słowa, wnet się gorszy.
Sai dai da yake ba shi da saiwa, yakan ɗan jima kaɗan kawai. Da wata wahala ko tsanani ya auko masa saboda maganar, nan da nan sai yă ja da baya.
22 A między ciernie posiany, ten jest, który słucha słowa; ale pieczołowanie świata tego i omamienie bogactw zadusza słowo, i staje się bez pożytku. (aiōn )
Wanda ya karɓi irin da ya fāɗi cikin ƙaya kuwa, shi ne mutumin da yakan ji maganar, sai dai damuwoyin rayuwan nan da jarrabar arzikin duniya sukan shaƙe shi, yă sa maganar ta kāsa amfani. (aiōn )
23 A na dobrej ziemi posiany, jest ten, który słucha słowa i rozumie, tenci pożytek przynosi; a przynosi jeden setny, drugi sześćdziesiątny, a drugi trzydziestny.
Amma wanda ya karɓi irin da ya fāɗi a ƙasa mai kyau, shi ne mutumin da yakan ji maganar yă kuwa fahimce ta. Yakan ba da amfani wani riɓi ɗari, sittin, ko talatin na abin da aka shuka.”
24 Drugie podobieństwo przełożył im, mówiąc: Podobne jest królestwo niebieskie człowiekowi, rozsiewającemu dobre nasienie na roli swojej.
Yesu ya ba su wani misali. “Mulkin sama yana kama da wani da ya shuka iri mai kyau a cikin gonarsa.
25 A gdy ludzie zasnęli, przyszedł nieprzyjaciel jego, i nasiał kąkolu między pszenicą, i odszedł.
Amma yayinda kowa yake barci, abokin gābansa ya zo ya yafa ciyayi a cikin alkamar, ya tafi abinsa.
26 A gdy urosła trawa i pożytek przyniosła, tedy się pokazał i kąkol.
Sa’ad da alkamar ta tashi ta yi kawuna, sai ciyayin ma suka bayyana.
27 Tedy przystąpiwszy słudzy gospodarscy, rzekli mu: Panie! izaliś dobrego nasienia nie nasiał na roli twojej? Skądże tedy ma kąkol?
“Bayin mai gonar suka zo wurinsa suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ashe, ba iri mai kyau ka shuka a gonarka ba? To, ina ciyayin nan suka fito?’
28 A on im rzekł: Nieprzyjaciel człowiek to uczynił. I rzekli słudzy do niego: A chceszże, iż pójdziemy, a zbierzemy go?
“Sai ya ce, ‘Abokin gāba ne ya yi wannan.’ “Bayin suka tambaye shi suka ce, ‘Kana so mu je mu tuttumɓuke su?’
29 A on rzekł: Nie! byście snać zbierając kąkol, nie wykorzenili zaraz z nim i pszenicy.
“Ya amsa ya ce, ‘A’a, don kada garin tuttumɓuke ciyayi, ku cire har da alkamar.
30 Dopuśćcie obojgu społem rość aż do żniwa; a czasu żniwa rzekę żeńcom: Zbierzcie pierwej kąkol, a zwiążcie go w snopki ku spaleniu; ale pszenicę zgromadźcie do gumna mojego.
Ku ƙyale su su yi girma tare sai lokacin girbi. A lokacin zan gaya wa masu girbi, da fari ku tara ciyayin ku kuma daure su dami-dami don a ƙone; sa’an nan ku tara alkamar ku kuma kawo su cikin rumbuna.’”
31 Insze podobieństwo przełożył im, mówiąc: Podobne jest królestwo niebieskie ziarnu gorczycznemu, które wziąwszy człowiek, wsiał na roli swojej.
Ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da ƙwayar mustad, wadda mutum ya ɗauka ya shuka a gonarsa.
32 Które najmniejszeć jest ze wszystkich nasion; ale kiedy urośnie, największe jest ze wszystkich jarzyn, i staje się drzewem, tak iż ptaki niebieskie przylatując, gniazda sobie czynią na gałązkach jego.
Ko da yake ita ce mafi ƙanƙanta cikin ƙwayoyinku, duk da haka sa’ad da ta yi girma, takan zama mafi girma cikin tsire-tsiren lambu ta kuma zama itace, har tsuntsayen sararin sama su zo su yi sheƙa a rassansa.”
33 Insze podobieństwo powiedział im: Podobne jest królestwo niebieskie kwasowi, który wziąwszy niewiasta, zakryła we trzy miary mąki, ażby wszystka skwaśniała.
Har yanzu ya ba su wani misali ya ce, “Mulkin sama yana kama da yisti wanda mace ta ɗauka ta kwaɓa garin alkama mai yawa, har sai da yistin ya gauraye yistin duka.”
34 To wszystko mówił Jezus w podobieństwach do ludu, a bez podobieństwa nie mówił do nich;
Yesu ya faɗa wa taron dukan waɗannan abubuwa cikin misalai; bai faɗa musu kome ba, sai tare da yin amfani da misalai.
35 Aby się wypełniło, co powiedziano przez proroka mówiącego: Otworzę w podobieństwach usta moje, wypowiem skryte rzeczy od założenia świata.
Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta wurin annabi cewa, “Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi abubuwan da suke ɓoye tun halittar duniya.”
36 Tedy rozpuściwszy on lud, przyszedł Jezus do domu; i przystąpili do niego uczniowie jego, mówiąc: Wyłóż nam podobieństwo o kąkolu onej roli.
Sa’an nan ya bar taron ya shiga gida. Almajiransa kuwa suka zo wurinsa suka ce, “Bayyana mana misalin ciyayin nan a gona.”
37 A on odpowiadając, rzekł im: Ten, który rozsiewa dobre nasienie, jest Syn człowieczy;
Ya amsa ya ce, “Mai yafa irin mai kyan nan, shi ne Ɗan Mutum.
38 A rola jest świat, a dobre nasienie są synowie królestwa; ale kąkol są synowie onego złego;
Gonar kuwa ita ce duniya, irin nan mai kyau kuwa suna a matsayin’ya’yan mulkin. Ciyayin nan kuma su ne’ya’yan mugun nan,
39 Nieprzyjaciel zasię, który go rozsiał, jestci dyjabeł, a żniwo jest dokonanie świata, a żeńcy są Aniołowie. (aiōn )
abokin gāban da yake shuka su kuwa, Iblis ne. Lokacin girbi kuma shi ne ƙarshen zamani, masu girbin kuwa su ne mala’iku. (aiōn )
40 Jako tedy zbierają kąkol, a palą go ogniem, tak będzie przy dokonaniu świata tego. (aiōn )
“Kamar yadda aka tattara ciyayin aka kuma ƙone a wuta, haka zai zama a ƙarshen zamani. (aiōn )
41 Pośle Syn człowieczy Anioły swoje, a oni zbiorą z królestwa jego wszystkie zgorszenia, i te, którzy nieprawość czynią;
Ɗan Mutum zai aiki mala’ikunsa, su kuwa cire daga mulkinsa kome da yake jawo zunubi da kuma duk masu aikata mugunta.
42 I wrzucą je w piec ognisty, tam będzie płacz i zgrzytanie zębów.
Za su jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
43 Tedy sprawiedliwi lśnić się będą jako słońce w królestwie Ojca swego. Kto ma uszy ku słuchaniu, niechaj słucha.
Sa’an nan masu adalci za su haskaka kamar rana a mulkin Ubansu. Duk mai kunnen ji, yă ji.”
44 Zasię podobne jest królestwo niebieskie skarbowi skrytemu w roli, który znalazłszy człowiek skrył, i od radości, którą miał z niego, odchodzi, i wszystko, co ma, sprzedaje, i kupuje onę rolę.
“Mulkin sama yana kama da dukiyar da aka ɓoye a gona. Da wani ya same ta, sai yă sāke ɓoye ta, sa’an nan cikin farin cikinsa yă je yă sayar da duk abin da yake da shi yă sayi gonar.
45 Zasię podobne jest królestwo niebieskie człowiekowi kupcowi, szukającemu pięknych pereł;
“Har wa yau dai, mulkin sama yana kama da ɗan kasuwa mai neman lu’ulu’ai masu kyau.
46 Który znalazłszy jednę perłę bardzo drogą, odszedł, i posprzedawał wszystko, co miał, i kupił ją.
Da ya sami dutse guda mai daraja sosai, sai ya tafi ya sayar da dukan abin da yake da shi ya saye shi.
47 Zasię podobne jest królestwo niebieskie niewodowi zapuszczonemu w morze, i ryby wszelkiego rodzaju zagarniającemu.
“Har yanzu, mulkin sama yana kama da abin kamun kifin da aka jefa cikin tafki yă kamo kifi iri-iri.
48 Który gdy był pełen, wyciągnęli rybitwi na brzeg, a usiadłszy, wybierali dobre ryby w naczynia, a złe precz wyrzucali.
Da abin kamun kifi ya cika, masuntan suka jawo shi gaci. Sai suka zauna suka tattara kifi masu kyau a kwanduna, amma suka zubar da marasa kyau.
49 Takci będzie przy dokonaniu świata; wynijdą Aniołowie, i wyłączą złe z pośrodku sprawiedliwych, (aiōn )
Haka zai kasance a ƙarshen zamani. Mala’iku za su zo su ware masu mugunta daga masu adalci (aiōn )
50 I wrzucą je w piec ognisty; tam będzie płacz i zgrzytanie zębów.
su kuma jefa su cikin wuta mai zafi, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”
51 Rzekł im Jezus: Wyrozumieliście to wszystko? Rzekli mu: Tak, Panie!
Yesu ya tambaye su ya ce, “Kun gane dukan waɗannan abubuwa?” Suka amsa, “I.”
52 A on im rzekł: Przetoż każdy nauczony w Piśmie, wyćwiczony w królestwie niebieskiem, podobny jest człowiekowi gospodarzowi, który wynosi z skarbu swego nowe i stare rzeczy.
Sa’an nan ya ce musu, “Saboda haka duk malamin dokokin da ya horu game da koyarwar mulkin sama, yana kama da maigida wanda yakan fitar daga ɗakin ajiyarsa sababbin dukiya da kuma tsofaffi.”
53 I stało się, gdy Jezus dokończył tych podobieństw, puścił się stamtąd.
Sa’ad da Yesu ya gama ba da waɗannan misalai, sai ya ci gaba daga can.
54 A przyszedłszy do ojczyzny swojej, nauczał je w bóżnicy ich, tak iż się bardzo zdumiewali i mówili: Skądże temu ta mądrość, i ta moc?
Yana isowa garinsa, sai ya fara koya wa mutane a cikin majami’arsu, suka kuwa yi mamaki. Suka yi ta tambaya suna cewa, “Ina wannan mutum ya sami irin wannan hikima da kuma ayyukan banmamaki haka?
55 Izaż ten nie jest on syn cieśli? Izaż matki jego nie zowią Maryją, a bracia jego Jakób, i Jozes, i Szymon, i Judas?
Wannan ba shi ne ɗan kafinta nan ba? Ba mahaifiyarsa ba ce Maryamu,’yan’uwansa kuma Yaƙub, Yusuf, Siman da Yahuda ba?
56 A siostry jego izali wszystkie u nas nie są? Skądże tedy temu to wszystko?
Duk’yan’uwansa mata kuma ba tare da mu suke ba? To, a ina wannan mutum ya sami dukan waɗannan abubuwa?”
57 I gorszyli się z niego; ale Jezus rzekł im: Nie jest prorok beze czci, tylko w ojczyźnie swojej i w domu swoim.
Sai suka ji haushinsa. Amma Yesu ya ce musu, “Sai a garinsa da kuma a gidansa na kaɗai annabi ba ya samun girma.”
58 I nie uczynił tam wiele cudów dla niedowiarstwa ich.
Bai kuwa yi abubuwan banmamaki da yawa a can ba saboda rashin bangaskiyarsu.