< Galacjan 4 >
1 Mówię tedy: (bracia!) Pokąd dziedzic jest dziecięciem, nic nie jest różny od sługi, panem będąc wszystkiego;
Abin da nake nufi shi ne, muddin magāji yana ɗan yaro ne tukuna, babu bambanci tsakaninsa da bawa, ko da yake shi ne da mallakar kome.
2 Ale jest pod opiekunami i dozorcami aż do czasu zamierzenia ojcowskiego.
Yana ƙarƙashin iyayen goyonsa da masu riƙon amana har yă zuwa cikar lokacin da mahaifinsa ya sa.
3 Także i my, gdyśmy byli dziećmi, pod żywioły świata byliśmy zniewoleni.
Haka yake, sa’ad da muke’yan yara, mun kasance cikin bauta a ƙarƙashin ƙa’idodin duniya.
4 Lecz gdy przyszło wypełnienie czasu, posłał Bóg onego Syna swego, który się urodził z niewiasty, który się stał pod zakonem,
Amma da lokacin da aka tsara ya yi sosai, sai Allah ya aiki Ɗansa, haifaffe daga mace, haifaffe a ƙarƙashin Doka,
5 Aby tych, którzy pod zakonem byli, wykupił, żebyśmy prawa przysposobienia za synów dostąpili.
domin yă fanshi waɗanda suke a ƙarƙashin doka, saboda mu sami cikakken matsayin zaman’ya’ya.
6 A iżeście synowie, przetoż posłał Bóg Ducha Syna swego w serca wasze, wołającego Abba, to jest Ojcze.
Da yake ku’ya’ya ne, sai Allah ya aiko da Ruhun Ɗansa a cikin zukatanmu, Ruhun da yake kira, “Abba, Uba.”
7 A tak już więcej nie jesteś niewolnikiem, ale synem; a ponieważ synem, tedy i dziedzicem Bożym przez Chrystusa.
Saboda haka kai ba bawa ba ne kuma, kai ɗa ne; da yake kuwa kai ɗa ne, Allah ya mai da kai magāji.
8 Aleć naonczas nie znając Boga, służyliście tym, którzy z przyrodzenia nie są bogowie.
Dā da ba ku san Allah ba, ku bayi ne ga waɗanda a ainihi ba alloli ba ne.
9 A teraz poznawszy Boga, owszem i poznani będąc od Boga, jakoż się zaś nazad wracacie ku żywiołom mdłym i mizernym, którym zasię znowu służyć chcecie?
Amma yanzu da kuka san Allah, ko kuma a ce Allah ya san ku, yaya kuke sāke komawa ga ƙa’idodin duniya marasa ƙarfi, abin tausayi kuma? Kuna so ku sāke komawa ga bautarsu ne?
10 Przestrzegacie dni i miesiące, i czasy, i lata.
Kuna kiyaye ranaku da watanni da lokuta da shekaru na musamman!
11 Boję się o was, bym snać darmo nie pracował około was.
Kai, kun ba ni tsoro, don ya zama kamar duk wahalar da na yi a kanku banza ne!
12 Bądźcie jako ja, gdyżem i ja jest jako wy, bracia! proszę was. W niczemeście mnie nie ukrzywdzili.
Ina roƙonku’yan’uwa, ku zama kamar ni, gama na zama kamar ku. Ba ku yi mini wani laifi ba.
13 Bo wiecie, żem w słabości ciała wam z przodku Ewangieliję opowiadał.
Kun san rashin lafiyar da na yi, shi ne ya yi mini hanyar da na kawo muku bishara da farko.
14 A pokuszenia mego, które było w ciele mojem, sobie nie lekceważyliście, aniście niem gardzili, aleście mię jako Anioła Bożego przyjęli i jako Chrystusa Jezusa.
Ko da yake ciwona gwaji ne gare ku, ba ku yi mini reni ko ƙyama ba. A maimakon haka, kuka karɓe ni sai ka ce mala’ikan Allah, kuma sai ka ce Kiristi Yesu kansa.
15 Jakież tedy było błogosławieństwo wasze? albowiem wam daję świadectwo, iż, by była rzecz można, dalibyście mi byli wyłupiwszy oczy wasze.
Me ya faru da dukan farin cikinku? Na tabbata, a lokacin, da mai yiwuwa ne da kun ciccire idanunku kun ba ni.
16 Takżem się stał nieprzyjacielem waszym, prawdę wam mówiąc?
Yanzu na zama abokin gābanku don na faɗa muku gaskiya ke nan?
17 Pałają ku wam miłością nie dobrze, owszem chcą was odstrychnąć, abyście ich miłowali.
Waɗancan mutane suna neman su rinjaye ku da ƙwazo, amma ba da kyakkyawar aniya ba. Abin da suke so shi ne su raba ku da mu, saboda ƙwazonku yă koma gare su.
18 A dobrać rzecz, pałać miłością w dobrem zawsze, a nie tylko, gdym jest obecnym u was.
Yana da kyau ku kasance da irin wannan niyya idan da nufi mai kyau ne, ku kuma kasance a haka koyaushe ba sai ina tare da ku ba.
19 Dziatki moje! (które znowu z boleścią rodzę, ażby Chrystus był wykształtowany w was),
Ya ku’ya’yana ƙaunatattu, ina sāke shan wahalar naƙudarku, har sai Kiristi ya kahu a cikinku.
20 Chciałbym teraz być u was i odmienić głos mój, ponieważ wątpię o was.
Da ma a ce ina tare da ku yanzu in canja muryata mana! Gama na damu ƙwarai saboda ku!
21 Powiedzcie mi, którzy pod zakonem chcecie być, nie słuchacież zakonu?
Ku gaya mini, ku da kuke so ku zauna a ƙarƙashin Doka, ba ku san abin da Doka ta ce ba ne?
22 Albowiem napisane, iż Abraham miał dwóch synów, jednego z niewolnicy, a drugiego z wolnej.
Gama a rubuce yake cewa Ibrahim yana da’ya’ya biyu maza, ɗaya ta wurin mace’yar aikin gidansa, ɗaya kuma ta wurin ainihin matarsa.
23 Lecz ten, który był z niewolnicy, według ciała się urodził, a który z wolnej, według obietnicy.
Ɗansa na wajen mace’yar aikin gidansa ya zo bisa ga ƙa’idar jiki ne; amma ɗansa na wajen ainihin matarsa ya zo a sakamakon alkawarin ne.
24 Przez co znaczą się insze rzeczy; albowiem te są one dwa testamenty; jeden z góry Synajskiej, który rodzi w niewolę; a ten jest jako Agar.
Za a iya ɗaukan waɗannan al’amura a matsayin misali, domin matan nan suna misalta alkawura biyu ne. Alkawari ɗaya daga Dutsen Sinai ne yana kuma haihuwar’ya’yan da za su zama bayi. Hagar ke nan.
25 Albowiem Agar jest góra Synaj w Arabii, a stosuje się do niej teraźniejsze Jeruzalem; bo jest w niewoli z dziatkami swojemi.
Hagar tana a matsayin Dutsen Sinai a Arabiya tana kuma kwatancin birnin Urushalima na yanzu, gama ita baiwa ce tare da’ya’yanta.
26 Lecz ono górne Jeruzalem wolne jest, które jest matką wszystkich nas.
Amma Urushalimar da take sama’yantacciya ce, ita ce kuma mahaifiyarmu.
27 Albowiem napisano: Rozwesel się niepłodna, która nie rodzisz; porwij się, a zawołaj, która nie pracujesz w porodzeniu; bo ta opuszczona wiele ma dziatek, więcej niż ta, która ma męża.
Gama a rubuce yake cewa, “Ki yi farin ciki, ya ke bakararriya, wadda ba ta haihuwa ki ɓarke da murna, ki kuma tā da murya, ke da ba kya naƙuda; domin da yawa ne’ya’yan macen da aka yashe, fiye da na mai miji.”
28 My tedy, bracia! tak jako Izaak, jesteśmy dziatkami obietnicy.
To, ku’yan’uwa, ku’ya’yan alkawari ne kamar Ishaku.
29 Ale jako na on czas ten, który się był urodził według ciała, prześladował tego, który się był urodził według ducha, tak się dzieje i teraz.
A wancan lokaci, wannan ɗa wanda aka haifa ta wurin ƙa’idar jiki ya tsananta wa wanda aka haifa ta ikon Ruhu. Haka ma yake har yanzu.
30 Ale co mówi Pismo? Wyrzuć niewolnicę i syna jej; albowiem nie będzie dziedziczył syn niewolnicy z synem wolnej,
Amma me Nassi ya ce? Nassi ya ce, “Kori macen nan’yar aikin gida da ɗanta don ɗan mace’yar aikin gida ba zai taɓa raba gādo tare da ɗa na ainihin matarka ba.”
31 A tak, bracia! nie jesteśmy dziećmi niewolnicy, ale wolnej.
Saboda haka,’yan’uwa, mu ba’ya’yan mace’yar aikin gida ba ne, amma na ainihin matan gidan ne.