< I Jana 2 >
1 Dziatki moje! to wam piszę, abyście nie grzeszyli; i jeźliby kto zgrzeszył, mamy orędownika u Ojca, Jezusa Chrystusa sprawiedliwego;
’Ya’yana ƙaunatattu, ina rubuta muku wannan ne don kada ku yi zunubi. Amma in wani ya yi zunubi, muna da wani wanda yake magana da Uba don taimakonmu, wato, Yesu Kiristi, Mai Adalci.
2 A on jest ubłaganiem za grzechy nasze; a nie tylko za nasze, ale też za grzechy wszystkiego świata.
Shi ne hadayar kafara saboda zunubanmu, kuma ba don namu kaɗai ba amma har ma da zunuban duniya duka.
3 A przez to wiemy, żeśmy go poznali, jeźli przykazania jego zachowujemy.
Ta haka za mu tabbata cewa mun san shi in muna yin biyayya da umarnansa.
4 Kto mówi: Znam go, a przykazania jego nie zachowuje, kłamcą jest, a prawdy w nim nie masz.
Mutumin da ya ce, “Na san shi,” amma ba ya yin abin da ya umarta, maƙaryaci ne, gaskiya kuwa ba ta cikinsa.
5 Lecz kto by zachował słowa jego, prawdziwie się w tym miłość Boża wykonała; przez to znamy, iż w nim jesteśmy.
Amma in wani ya yi biyayya da maganarsa, ƙaunar Allah ta zama cikakkiya ke nan a cikinsa. Ta haka muka san cewa muna cikinsa.
6 Kto mówi, że w nim mieszka, powinien, jako on chodził, i sam także chodzić.
Duk wanda ya ce yana rayuwa a cikinsa dole yă yi tafiya kamar yadda Yesu ya yi.
7 Bracia! nie nowe przykazanie wam piszę, ale przykazanie stare, któreście mieli od początku; a to stare przykazanie jest ono słowo, któreście słyszeli od początku.
Abokaina ƙaunatattu, ba sabon umarni nake rubuta muku ba, a’a, daɗaɗɗen umarnin nan ne, wanda kuke da shi tun farko. Wannan tsohon umarni shi ne saƙon da kuka riga kuka ji.
8 Zasię przykazanie nowe piszę wam, które jest prawdziwe w nim i w was; iż ciemność przemija, a prawdziwa ona światłość już świeci.
Duk da haka ina rubuta muku sabon umarni; ana ganin gaskiyar umarnin a cikinsa da kuma cikinku, gama duhu yana shuɗewa, haske na gaskiya kuwa yana haskakawa.
9 Kto mówi, iż jest w światłości, a brata swego nienawidzi, w ciemności jest aż dotąd.
Duk wanda ya ce yana cikin haske yana kuma ƙin ɗan’uwansa, ashe a duhu yake har yanzu.
10 Kto miłuje brata swego, w światłości mieszka i zgorszenia w nim nie masz.
Duk wanda yake ƙaunar ɗan’uwansa, a cikin hasken yake rayuwa ke nan, kuma babu wani abin da yake cikinsa da zai sa yă yi tuntuɓe.
11 Lecz kto nienawidzi brata swego, w ciemności jest i w ciemności chodzi, a nie wie, gdzie idzie, iż ciemność zaślepiła oczy jego.
Amma duk wanda yake ƙin ɗan’uwansa, cikin duhu yake, yana kuma tafiya cikin duhu ke nan; bai ma san inda za shi ba, domin duhun ya makanta shi.
12 Piszę wam, dziatki! iż wam są odpuszczone grzechy dla imienia jego.
Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin an gafarta muku zunubanku saboda sunansa.
13 Piszę wam, ojcowie! żeście poznali tego, który jest od początku. Piszę wam, młodzieńcy! żeście zwyciężyli onego złośnika.
Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kun ci nasara a kan mugun nan.
14 Piszę wam, dziateczki! żeście poznali Ojca. Pisałem wam, ojcowie! żeście poznali onego, który jest od początku. Pisałem wam, młodzieńcy! że jesteście mocni, a słowo Boże mieszka w was, a żeście zwyciężyli onego złośnika.
Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin kun san Uba. Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kuna da ƙarfi, maganar Allah kuwa tana zaune a cikinku, kun kuma ci nasara a kan mugun nan.
15 Nie miłujcie świata, ani tych rzeczy, które są na świecie; jeźli kto miłuje świat, nie masz w nim miłości ojcowskiej.
Kada ku ƙaunaci duniya, ko wani abin da yake cikinta. In wani yana ƙaunar duniya, ƙaunar Uba ba ta cikinsa.
16 Albowiem wszystko, co jest na świecie, jako pożądliwość ciała i pożądliwość oczu, i pycha żywota, toć nie jest z Ojca, ale jest z świata.
Gama duk abin da yake na duniya, kamar sha’awace-sha’awacen mutuntaka, sha’awar idanunsa, da kuma taƙama da abin da yake da shi, yake kuma yi, ba daga wurin Uba suke fitowa ba sai dai daga duniya.
17 Światci przemija i pożądliwość jego; ale kto czyni wolę Bożą, trwa na wieki. (aiōn )
Duniya da sha’awace-sha’awacenta suna shuɗewa, amma mutumin da yake aikata nufin Allah, zai rayu har abada. (aiōn )
18 Dziateczki! ostateczna godzina jest; a jakoście słyszeli, że antychryst przyjść ma, i teraz wiele antychrystów powstało; stąd wiemy, iż jest ostateczna godzina.
’Ya’yana ƙaunatattu, waɗannan su ne kwanakin ƙarshe; kuma kamar yadda kuka ji cewa magabcin Kiristi yana zuwa, ko yanzu ma abokan gāban Kiristi da yawa sun zo. Ta haka muka san cewa kwanakin ƙarshe sun iso.
19 Z nas wyszli, ale nie byli z nas; albowiem gdyby byli z nas, zostaliby byli z nami; ale wyszli z nas, aby objawieni byli, iż wszyscy nie byli z nas.
Waɗannan masu gāba da Kiristi suna cikinmu a dā, amma sun bar mu, don tun dā ma su ba namu ba ne. Ai, da su namu ne, da har yanzu suna tare da mu. Amma sun bar mu, wannan ya nuna a fili cewa su ba namu ba ne.
20 Ale wy macie pomazanie od onego Świętego i wiecie wszystko.
Amma ku kam, kuna da shafewa daga wurin Mai Tsarkin nan, kuma dukanku kun san gaskiya.
21 Nie pisałem wam, przeto żeście prawdy nie znali, ale że ją znacie, a iż wszelkie kłamstwo nie jest z prawdy.
Ina rubuta muku ba domin ba ku san gaskiya ba ne, a’a, sai dai domin kun santa, kun kuma san cewa babu yadda ƙarya za tă fito daga gaskiya.
22 Kto jest kłamcą? Azaż nie ten, który zapiera, iż Jezus nie jest Chrystusem? Ten jest antychryst, który się zapiera Ojca i Syna.
Wane ne maƙaryaci? Ai, shi ne mutumin da yake mūsun cewa Yesu shi ne Kiristi. Irin wannan mutum shi ne magabcin Kiristi, ya yi mūsun Uban da kuma Ɗan.
23 Każdy, co się zapiera Syna, i Ojca nie ma; a kto wyznaje Syna, ma i Ojca.
Ba wanda yake mūsun Ɗan, sa’an nan yă ce yana da Uban; duk wanda ya yarda da Ɗan, yana da Uban a cikinsa ke nan.
24 Wy tedy, coście słyszeli od początku, to niechaj w was zostaje; jeźliby w was zostawało, coście słyszeli od początku, i wy w Synu i w Ojcu zostaniecie.
Ku lura fa cewa abin da kuka ji daga farko, bari yă ci gaba da kasance a cikinku. In kuwa ya ci gaba da zama a cikinku, za ku kasance a cikin Ɗan, da kuma a cikin Uban.
25 A tać jest obietnica, którą on nam obiecał, to jest żywot on wieczny. (aiōnios )
Wannan shi ne abin da ya yi mana alkawari, wato, rai madawwami. (aiōnios )
26 Tom wam napisał o tych, którzy was zwodzą.
Ina rubuta muku waɗannan abubuwa ne game da waɗanda suke ƙoƙari su sa ku kauce.
27 Ale to pomazanie, któreście wy wzięli od niego, zostaje w was, a nie potrzebujecie, aby was kto uczył: ale jako to pomazanie uczy was o wszystkiem, a jest prawdziwe, i nie jest kłamstwem, a jako was nauczyło, tak w niem zostaniecie.
Game da ku kuwa, shafan nan da kuka karɓa daga gare shi tana nan a cikinku, ba kwa kuma bukata wani yă koyar da ku. Amma kamar yadda shafan nan tasa tana koya muku kome, ita kuwa gaskiya ce ba ƙarya ba, yadda dai ta koya muku, to, sai ku zauna a cikinsa.
28 I teraz, dziateczki! zostańcie w niem, abyśmy, gdy się ukaże, ufanie mieli, a nie byli zawstydzeni od niego w przyjściu jego.
Yanzu fa, ya ku’ya’yana ƙaunatattu, sai ku ci gaba a cikinsa, domin sa’ad da ya bayyana, mu iya tsaya gabagadi babu kunya a dawowarsa.
29 Ponieważ wiecie, że on sprawiedliwy jest, wiedzcież też, iż każdy, który czyni sprawiedliwość, z niego narodzony jest.
In kun san cewa shi mai adalci ne, to, kun dai san cewa duk mai aikata abin da yake daidai haifaffensa ne.