< I Koryntian 3 >
1 I ja, bracia! nie mogłem wam mówić jako duchownym, ale jako cielesnym i jako niemowlątkom w Chrystusie.
’Yan’uwa, ban iya yi muku magana kamar masu ruhaniya ba, sai dai kamar masu halin mutuntaka, jarirai cikin bin Kiristi kawai.
2 Napawałem was mlekiem, a nie karmiłem was pokarmem; boście jeszcze nie mogli znieść, owszem i teraz jeszcze nie możecie,
Na ba ku madara ba abinci mai tauri ba, domin ba ku balaga ba a lokacin. Kai, har yanzu ma, ba ku balaga ba.
3 Gdyż jeszcze cielesnymi jesteście. Bo ponieważ między wami jest zazdrość i swary, i rozterki, azażeście nie cieleśni i według człowieka nie chodzicie?
Har yanzu kuna rayuwa bisa ga halin mutuntaka. Da yake akwai kishi da faɗace-faɗace a cikinku, ba rayuwa irin ta halin mutuntaka ke nan kuke yi ba? Kuma ba rayuwa irin ta mutane ce kawai kuke yi ba?
4 Albowiem gdy kto mówi: Jam jest Pawłowy, a drugi: Jam Apollosowy, azaż cielesnymi nie jesteście?
Gama sa’ad da wani ya ce, “Ni na Bulus ne,” wani kuma ya ce, “Ni na Afollos ne,” ba rayuwa irin ta mutane ke nan kuke yi ba?
5 Bo któż jest, Paweł? Kto Apollos? jedno słudzy, przez którycheście uwierzyli, a to jako każdemu Pan dał.
Shin, wane ne Afollos? Wane ne kuma Bulus? Ai, bayi ne kawai waɗanda ta wurinsu kuka gaskata, kamar yadda Ubangiji ya ba kowannensu aikinsa.
6 Jam szczepił, Apollos polewał, ale Bóg wzrost dał.
Ni na shuka iri, Afollos kuma ya yi banruwa, amma Allah ne ya sa irin ya yi girma.
7 A tak, ani ten, co szczepi, jest czem, ani ten, co polewa, ale Bóg, który wzrost daje.
Don haka, da wanda ya yi shuki, da wanda ya yi banruwa, ba a bakin kome suke ba, sai dai Allah kaɗai, mai sa abubuwa su yi girma.
8 Lecz ten, który szczepi, i ten, który polewa, jedno są, a każdy swoję zapłatę weźmie według pracy swojej.
Mutumin da ya yi shuki, da mutumin da ya yi banruwa nufinsu ɗaya ne, kuma kowannensu zai sami lada gwargwadon aikinsa.
9 Albowiem jesteśmy pomocnikami Bożymi, wy Bożą rolą, Bożym budynkiem jesteście.
Gama mu abokan aiki ne na Allah; ku kuwa gonar ce ta Allah, ginin Allah kuma.
10 Według łaski Bożej, która mi jest dana, jako mądry budownik założyłem grunt, a drugi na nim buduje: wszakże każdy niechaj baczy, jako na nim buduje.
Ta wurin alherin da Allah ya ba ni, na kafa tushen gini kamar ƙwararren magini, wani kuma dabam yana gini a kai. Amma kowa yă lura da yadda yake gini.
11 Albowiem gruntu innego nikt nie może założyć, oprócz tego, który jest założony, który jest Jezus Chrystus.
Gama babu wanda zai iya kafa wani tushen gini dabam da wanda aka riga aka kafa, wanda yake Yesu Kiristi.
12 A jeźli kto na tym gruncie buduje złoto, srebro, kamienie drogie, drwa, siano, słomę,
In wani ya yi gini a kan tushen ginin nan da zinariya, azurfa, duwatsu masu daraja, itace, ciyawa ko kara,
13 Każdego robota jawna będzie; bo to dzień pokaże, gdyż przez ogień objawiona będzie, a każdego roboty, jaka jest, ogień doświadczy.
aikin zai bayyana kansa, domin za a nuna shi a sarari a Ranar. Wuta ce za tă bayyana aikin, wutar kuwa za tă gwada ingancin aikin kowa.
14 Jeźli czyja robota zostanie, którą na nim budował, zapłatę weźmie.
In abin da kowane mutum ya gina ya tsaya, zai sami lada.
15 Jeźli czyja robota zgore, ten szkodę podejmie; lecz on sam będzie zachowany, wszakże tak jako przez ogień.
In ya ƙone, zai yi hasara, amma zai sami ceto, sai dai kamar wanda ya bi ta tsakiyar wuta ne.
16 Azaż nie wiecie, iż kościołem Bożym jesteście, a Duch Boży mieszka w was?
Ashe, ba ku sani ba cewa ku kanku haikalin Allah ne, Ruhun Allah kuma yana zaune a cikinku?
17 A jeźli kto gwałci kościół Boży, tego Bóg skazi, albowiem kościół Boży święty jest, którym wy jesteście.
Duk wanda ya ɓata haikalin Allah, Allah zai ɓata shi, don haikalin Allah mai tsarki ne, ku ne kuwa haikalin nan.
18 Niechajże nikt samego siebie nie zwodzi; jeźli się kto sobie zda być mądrym między wami na tym świecie, niech się stanie głupim, aby się stał mądrym. (aiōn )
Kada ku ruɗi kanku. In waninku yana tsammani cewa yana da hikima, yadda duniya ta ɗauki hikima, to, sai ya mai da kansa “wawa” don yă zama mai hikima. (aiōn )
19 Albowiem mądrość tego świata głupstwem jest u Boga; bo napisano: Który chwyta mądrych w chytrości ich;
Gama hikimar duniyan nan, wauta ce a gaban Allah, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Yakan kama masu hikima a cikin makircinsu”;
20 I zasię: Pan zna myśli mądrych, iż są marnością.
kuma a rubuce yake cewa, “Ubangiji ya san dukan tunanin masu hikima banza ne.”
21 A tak niech się nikt nie chlubi ludźmi; albowiem wszystkie rzeczy są wasze.
Saboda haka, kada wani yă yi taƙama da mutum! Gama kome naku ne,
22 Bądź Paweł, bądź Apollos, bądź Kiefas, bądź świat, bądź żywot, bądź śmierć, bądź przytomne, bądź przyszłe rzeczy, wszystkie są wasze;
ko Bulus ko Afollos ko Kefas ko duniya ko rai ko mutuwa ko abubuwa na yanzu ko na nan gaba, ai, duka naku ne,
23 Aleście wy Chrystusowi, a Chrystus Boży.
ku kuwa na Kiristi ne, Kiristi kuma na Allah ne.