< Lukas 20 >
1 KADEKADEO eu ran ni a kotin kawewe ong aramas akan nan im en kaudok o, o padaki rongamau, samero lapalap, o saunkawewe, iangaki saumas akan ap ko dong i.
Ana nan wata rana, Yesu yana kan koyarwa a haikali da wa'azin bishara, sai shugaban firistoci da marubuta suka zo wurinsa da dattawa.
2 Potoan ong i indada: Masani ong kit, manaman en is, me komui wiaki mepukat? De is me ki ong komui manaman wet?
Suka yi magana, su na ce masa, “Gaya mana da wanne iko ne ka ke yin wadannan abubuwan? Ko wanene ya baka wannan ikon?”
3 A kotin sapeng masani ong irail: I pil pan kalelapok meakot re omail, komail en sapeng ia!
Ya amsa sai ya ce masu, “Ni ma zan yi maku tambaya. Gaya mani game
4 En Ioanes a paptais men nanlang, de me ren aramas?
da baptisman Yahaya. Daga sama take ko kuwa daga mutane ne?”
5 Irail ap lamelame nan pung arail indada: Ma kitail pan inda, men nanlang, a pan masani ong kitail: Da me komail so posonki i?
Sai suka yi mahawara da junansu, suna cewa, “In mun ce, 'Daga sama,' zai ce, 'To don me ba ku ba da gaskiya gareshi ba?'
6 A ma kitail inda, me ren aramas, aramas karos ap pan kate kit, pwe re kin wia saukopki Ioanes.
Amma in mun ce, 'Daga mutane ne,' dukan mutane za su jejjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata a ransu Yahaya annabi ne.”
7 Irail ari sapeng, me re sasa, wasa me a kosang ia.
Sai suka amsa cewa ba su san ko daga ina ne take ba.
8 Iesus ap kotin masani ong irail: Ari, I pil sota pan indai ong komail, manaman en is, me I wiaki mepukat.
Yesu yace masu, “To haka ni ma ba zan gaya maku ko da wanne iko nake yin wadannan abubuwan ba.”
9 A ap kotin tapiada masani ong pokon o karaseras wet: Aramas amen padukedier mat en wain eu, ap liki ong saumat akai, o kokola nan wai ansau warai.
Ya gaya wa mutane wannan misali, “Wani mutum ya dasa gonar inabi, ya ba wadansu manoma jinginarta, sai ya tafi wata kasa har ya dade.
10 A lao ansau, a kadaralang saumat akan ladu men, pwe ren ki ong kisan wan wain. A saumat akan woki i, o kadarala i kaip.
Da lokacin girbi ya yi sai ya aiki wani bawansa zuwa wurin manoman, saboda su bashi daga cikin anfanin gonar. Amma manoman suka doke shi, sai suka kore shi hannu wofi.
11 A murin met a pil kadarala amen ladu, a re pil woki i, o wia suedi ong, o kadarala i kaip.
Ya aike wani bawa kuma sai suka daddoke shi, suka kunyatar da shi, suka kore shi hannu wofi.
12 A murin met a kadarala kasilimen. A re pil kame i o siken wei sang.
Ya kuma sake aike na uku suka yi masa rauni, suka jefar da shi a waje.
13 Monsap en mat en wain o ap masani: Da me i en wiada? I pan kadarala nai ol kompok, ele re pan masak, ni ar pan kilang i.
Sai mai gonar inabin ya ce, 'Me zan yi? Zan aiki kaunattacen dana. Watakila zasu ba shi daraja.'
14 A saumat akan lao kilanger i, rap lamelame nan pung ar indada: Iei i, me pan ale soso, kitail pan kamela, pwen id aneki a soso.
Amma sa'adda manoman suka gan shi, suka yi shawara a tsakaninsu, cewa, 'Wannan ne magajin. Bari mu kashe shi, saboda gadon ya zama namu.'
15 Irail lao kasapoka sang i nan matuel o, ap kamela i. Da me monsap en mat en wain pan wiai ong irail?
Suka jefar da shi waje daga gonar, suka kashe shi. Menene ubangijin gonar inabin zai yi da su?
16 A pan kodo kamela saumat pukat, ap liki ong akai a mat en wain. Irail lao ronger mepukat, rap indada: O mepukat sota pan wiaui!
Zai zo ya halakar da wadannan manoma, sai ya ba wadansu gonar.” Da suka ji wannan, suka ce, “Allah ya sawake!”
17 A kotin saupei wong irail ap kotin masani: Iaduen wewe en inting wet: Takai o, me sause kasapokela, id wiala takai en pukakaim?
Amma Yesu ya kalle su, sai yace, “Menene ma'anar wannan nassi? 'Dutsen da magina suka ki, an mayar da shi kan kusurwa'?
18 Meamen, me pupedi pon takai wet pan ola. A me a pupedi ong poa, a pan kapitaka pasang i.
Duk wanda ya fadi kan dutsen zai farfashe. Amma duk wanda dutsen ya fadi a kansa, zai rugurguza shi.”
19 I dokan o saunkawewe o samero lapalap akan raparapaki en saikidi i. A re masak aramas akan, pwe re muilikiada, me a karaseras kin irail.
Sai marubutan da manyan firistocin suka so su kama shi a wannan sa'a, domin sun sani ya yi wannan misali a kansu ne. Amma sun ji tsoron mutane.
20 Irail ari masamasan i o kadarala liparok kai, me pan wia kin pein irail aramas pung, pwe ren saikikidi i a masan akan ap pangalang saunkapung o manaman en kopina.
Suna fakonsa, suka aiki magewaya, wadanda suke kamar masu adalci, saboda su sami kuskure cikin maganarsa, don su mika shi ga hukumci da kuma ikon gwamna.
21 Irail ari kalelapok re a potoan ong: Saunpadak, kit potoan asa, me ar masan o padak kan me pung, o re sota kotin kupuroki sansal en aramas. Pwe re kin kotin kaukaweweda melel duen al en Kot.
Suka tambaye shi, cewa, “Malam, mun sani da cewa kana fada da koyar da abin ke daidai, kuma ba wanda yake cusa maka ra'ayi, amma kana koyar da gaskiya game da hanyar Allah.
22 Me pung kit en nopwei ong nanmarki, de so?
Wai shin doka ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
23 A i kotin mangi ar widing, ap masani ong ir: Da me komail kasongesong kin ia?
Amma Yesu ya gane makircinsu, sai ya ce masu,
24 Kasale dong ia denar eu! Mom en is o inting wet? Re sapeng potoan ong: En nanmarki.
“Nuna mani dinari. Sifar wanene da kuma rubutun wanene akan sa?” Suka ce, “Na Kaisar ne.”
25 A i kotin masani ong irail: Ari komail ki ong nanmarki, me nain nanmarki, o ong Kot, me sapwilim en Kot!
Sai ya ce masu, “To sai ku ba Kaisar abin da ke na Kaisar, ku kuma ba Allah, abin da ke na Allah.”
26 Irail ari sota kak saikikidi i a masan akan mon pokon o. Irail puriamuiki me a kotin sapeng, o nenenlata.
Marubutan da manyan firistocin ba su sami abin zargi cikin maganarsa, a gaban mutane ba. Suka yi mamakin amsar sa, ba su kuma ce komai ba.
27 Sadusär akai, me kin inda, me dene melar akan solar pan maureda, ap kai dong i kalelapok re a,
Sa'adda wadansu Sadukiyawa suka zo wurinsa, wadan da suka ce babu tashin mattatu,
28 Potoan ong: Saunpadak, Moses intingie dong kit, ma ri ol en amen pan mela, me a paud li dapwan men, ri a ol ap pan paudekida i, pwen kaipwi ong ri a ol na seri kai.
suka tambaye shi, cewa, “Malam, Musa ya rubuta mana cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, mai mace kuma ba shi da yaro, sai dan'uwansa ya auri matar, ya samar wa dan'uwansa yaro.
29 Ari, pwin pirien, ol isimen mia, men mas paudeki li amen, ap mela, a sota na seri ko.
Akwai 'yan'uwa guda bakwai kuma na farin ya yi aure, sai ya mutu babu da,
30 A kariamen paude kida li o ap mela a sota na seri ko.
haka ma na biyun.
31 A kasilimen paude kida i, iduen ir isimen karos, re mela, ap sota nairail seri ko.
Na ukun ya aure ta, haka nan na bakwai ma bai bar yaya ba, har suka mutu.
32 A ikmuri li o pil mela.
Daga baya sai matar ma ta mutu.
33 Ari, ni en me melar akan ar iasada, a pan en is a paud? Pwe ir isimen karos paude kida i.
To a ranar tashin mattatu, matar wa za ta zama? Domin duka bakwai din sun aure ta.”
34 Iesus kotin masani ong irail: Seri en sappa et kin papaud o kapapaud. (aiōn )
Yesu ya ce masu, “'Ya'yan duniyan nan suna aure, ana kuma ba da su ga aure. (aiōn )
35 A me war ong ale eu sap o konodi maureda sang ren me melar akan, re sota kin papaud de kapapaud. (aiōn )
Amma wadanda aka ga cancantarsu a waccan tsara, sun isa su sami tashin mattatu, ba za suyi aure ko a aurar da su ba. (aiōn )
36 Pwe re pil solar kak mela. Pwe re paroki ong tounlang kan, o re seri en Kot akan, pwe re seri en kamaur.
Gama ba za su mutu kuma ba, domin suna daidai da mala'iku kuma su 'ya'yan Allah ne, da shike su 'ya'yan tashin matattu ne.
37 A duen en me melar akan ar pan maureda, Moses pil kadededa, ni a udial tuka o, ni a kaadaneki Kaun o: Kot en Apraam, o Kot en Isaak, o Kot en Iakop.
Amma batun tashi matattu, ko Musa ma ya nuna wannan, a cikin jeji, inda ya kira Ubangiji, Allah na Ibrahim da kuma Allah na Ishaku da Allah na Yakubu.
38 Pwe Kot kaidin Kot en me melar akan, a en me maur akan, pwe karos memaur ong i.
Yanzu shi ba Allahn matattu ba ne, amma na masu rai, saboda duka suna raye a wurinsa.”
39 A Saunkawewe kai sapeng indada: Saunpadak, ar masan me pung.
Wadansu marubuta suka amsa, “Malam, ka amsa da kyau.”
40 Irail ap solar kak peidok re a okotme,
Gama ba su sake yi masa wadansu tambayoyi ba.
41 I ari kotin masani ong irail: Iaduen ar indinda, me Kristus nain Dawid?
Yesu ya ce masu, “Yaya suke cewa Almasihu dan Dauda ne?
42 A pein Dawid katitiki nan puk en Psalm: Kaun o kotin masani ong ai Kaun: Mondi ong ni pali maun i.
Gama Dauda da kansa ya ce a cikin littafin Zabura, Ubangiji ya ce wa Ubangiji na, 'Zauna a hannun dama na,
43 Lao I pan wia kida om imwintiti utepan nä om.
sai na maida makiyanka a karkashin tafin sawunka.'
44 Dawid ari wia kin i a Kaun, a iaduen a pan kak na ol?
Dauda ya kira Kristi 'Ubangiji', to ta yaya ya zama dan Dauda?”
45 A ni aramas karos rongadar, a kotin masani ong sapwilim a tounpadak kan:
Dukan mutane suna ji ya ce wa almajiransa,
46 Kalaka saunkawewe kan, me kin mauki momait sili nan likau reirei o mauki, aramas en ranamau ong irail nan wasa en netinet akan, o men mondi leppantam nan sinakoke kan o ni tapin tepel.
“Ku yi hankali da marubuta, wadanda suna son tafiya da manyan riguna, suna kuma son a gaishe su a cikin kasuwanni, da mayan wuraren zama a cikin majami'u, da kuma manyan wurare a wurin bukukkuwa.
47 Me kin ngopur im en li odi kan, liasoski kapakap reirei, mepukat pan pangalang kadeik apwal.
Suna kuma kwace wa gwamraye gidaje, suna kuma badda kama ta wurin yin doguwar addu'a. Wadannan za su sha hukumci mai girma.”