< زکریا 4 >
فرشتهای که با من صحبت میکرد، مرا مثل شخصی که خوابیده باشد، بیدار کرد. | 1 |
Sai mala’ikan da ya yi magana da ni ya komo ya farkar da ni, kamar yadda ake farkar da mutum daga barcinsa.
سپس از من پرسید: «چه میبینی؟» جواب دادم: «چراغدانی از طلا میبینم که هفت چراغ دارد و بر سر آن روغندانی هست که به وسیلۀ هفت لولهای که به آن متصل است به چراغها روغن میرساند. | 2 |
Ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, na ce, “Na ga wurin ajiye fitilan zinariya da kwano a kai, da kuma fitilu bakwai a kansa, da butocin kai wa fitilu mai guda bakwai.
همچنین دو درخت زیتون میبینم که یکی در طرف راست و دیگری در طرف چپ چراغدان قرار دارد.» | 3 |
Akwai kuma itatuwan zaitun guda biyu a gefensa, ɗaya a gefen dama na kwanon ɗaya kuma a gefen hagunsa.”
سپس از فرشته پرسیدم: «ای سرورم اینها چیستند و چه معنایی دارند؟» | 4 |
Na tambayi mala’ikan da ya yi magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
فرشته گفت: «آیا نمیدانی؟» گفتم: «نه، سرورم، نمیدانم.» | 5 |
Sai ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na amsa, na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
سپس فرشته گفت: «این است آنچه خداوند به زروبابِل میگوید: نه به قدرت، نه به قوت، بلکه به روح من؛ خداوند لشکرهای آسمان این را میگوید. | 6 |
Sai ya ce mini, “Wannan ce maganar Ubangiji ga Zerubbabel. ‘Ba ta wurin ƙarfi ba, ko ta wurin iko, sai dai ta wurin Ruhuna,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
ای زروبابِل، این کوه مشکلات در برابر تو فرو خواهد ریخت و وقتی تو آخرین سنگ بنای خانهٔ مرا گذاشتی، مردم فریاد خواهند زد: برکت خداوند بر آن باد!» | 7 |
“Kai mene ne, ya babban dutse? A gaban Zerubbabel za a rushe ka ka zama fili. Sa’an nan Zerubbabel yă kawo dutsen da ya fi kyau, a kuma yi ta sowa ana cewa, ‘Allah yă yi masa albarka! Allah yă yi masa albarka!’”
پیام دیگری از جانب خداوند بر من نازل شده، گفت: | 8 |
Sai maganar Ubangiji ta zo mini,
«دستهای زروبابِل این خانه را بنیاد نهاد و دستهای وی آن را تمام خواهد کرد. وقتی این کار انجام شود آنگاه قوم من خواهند دانست که خداوند، خدای لشکرهای آسمان مرا نزد شما فرستاده است. | 9 |
“Hannuwan Zerubbabel sun kafa harsashin haikalin nan; hannuwansa ne kuma za su gama ginin. Sa’an nan ne za ka san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni zuwa wurinka.
هر چند مردم از اینکه در کار بنای خانهٔ من پیشرفت چشمگیری حاصل نشده دلسردند، اما وقتی زروبابِل را مشغول کار ببینند، امیدوار خواهند شد.» | 10 |
“Wa ya rena ranar ƙananan abubuwa? Mutane za su yi murna sa’ad da suka ga igiyar gwaji a hannun Zerubbabel. “Waɗannan guda bakwai ɗin su ne idanun Ubangiji, masu jujjuyawa cikin dukan duniya.”
سپس از فرشته پرسیدم: «آن دو درخت زیتون دو طرف چراغدان | 11 |
Sai na tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan itatuwan zaitun guda biyu tsaye a hagu da kuma daman wurin ajiye fitilan fitilu?”
و آن دو شاخهٔ زیتون کنار دو لولهٔ طلا که از آنها روغن میریزد، چه هستند؟» | 12 |
Na sāke tambaye shi na ce, “Mene ne waɗannan rassa biyun nan na zaitun a gefen bututu biyu na zinariya da suke zuba man zinariya?”
گفت: «آیا نمیدانی؟» گفتم: «نه، سرورم، نمیدانم.» | 13 |
Ya amsa ya ce, “Ba ka san mene ne waɗannan ba?” Na ce, “A’a, ranka yă daɗe.”
آنگاه او به من گفت: «آنها نشانهٔ دو مردی هستند که خداوند، مالک تمامی جهان، آنها را برگزیده و مسح کرده تا او را خدمت کنند.» | 14 |
Sai ya ce, “Waɗannan su ne biyun da aka shafe don su yi wa Ubangiji dukan duniya hidima.”