< مزامیر 96 >

سرودی تازه در وصف خداوند بسرایید! ای همه مردم روی زمین در وصف خداوند بسرایید! 1
Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
در وصف خداوند بسرایید و نام او را حمد گویید. هر روز به مردم بشارت دهید که خداوند نجات می‌بخشد. 2
Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
شکوه و جلال او را در میان ملتها ذکر کنید، و از معجزات او در میان قومها سخن بگویید. 3
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
زیرا خداوند بزرگ است و سزاوار ستایش! از او باید ترسید، بیش از همۀ خدایان. 4
Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
خدایان سایر قومها بتهایی بیش نیستند، اما خداوند ما آسمانها را آفریده است. 5
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
شکوه و جلال در حضور اوست، و قدرت و شادمانی در قُدس او. 6
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
ای تمام قومهای روی زمین، خداوند را توصیف نمایید؛ قدرت و شکوه او را توصیف نمایید؛ 7
Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
عظمت نام خداوند را توصیف نمایید! با هدایا به خانۀ او بیایید. 8
Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
خداوند را در شکوه قدوسیتش بپرستید! ای تمامی مردم روی زمین، در حضور او بلرزید. 9
Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
به همه قومها بگویید «خداوند سلطنت می‌کند! جهان پایدار است و تکان نخواهد خورد. او قومها را با انصاف داوری خواهد کرد.» 10
Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
آسمان شادی کند و زمین به وجد آید، دریا و هر چه آن را پر می‌سازد، غرش کند؛ 11
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
صحرا و هر چه در آن است، شادمان گردد. درختان جنگل با شادی بسرایند، 12
bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
در حضور خداوند که برای داوری جهان می‌آید. او همه قومها را با عدل و انصاف داوری خواهد کرد. 13
za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.

< مزامیر 96 >