< مزامیر 94 >
ای خداوند، ای خدای انتقام گیرنده، قدرتت را نشان بده. | 1 |
Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
ای داور جهان، برخیز و متکبران را به سزای اعمالشان برسان. | 2 |
Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
گناهکاران تا به کی پیروز و سرافراز خواهند بود؟ | 3 |
Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
همهٔ بدکاران، گستاخ و ستمگر هستند و حرفهای ناروا میزنند. | 4 |
Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
قوم تو را از بین میبرند و بر بندگانت ظلم میکنند. | 5 |
Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
بیوهزنان و غریبان و یتیمان را میکشند. | 6 |
Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
این ستمکاران میگویند: «خداوند ما را نمیبیند و خدای یقعوب متوجهٔ کارهای ما نمیشود.» | 7 |
Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
ای قوم من، چرا اینقدر نادان هستید؟ کِی عاقل خواهید شد؟ | 8 |
Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
آیا خدا که به ما گوش داده است، خودش نمیشنود؟ او که به ما چشم داده است، آیا نمیبیند؟ | 9 |
Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
او که همهٔ قومها را مجازات میکند، آیا شما را مجازات نخواهد کرد؟ او که همه چیز را به انسان میآموزد، آیا نمیداند که شما چه میکنید؟ | 10 |
Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
خداوند از افکار انسان آگاه است و میداند که آنها پوچ و بیارزشاند. | 11 |
Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
خوشا به حال کسی که تو، ای خداوند، او را تأدیب میکنی و قوانین خود را به او میآموزی. | 12 |
Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
چنین شخصی، در روزهایی که تو گناهکاران را گرفتار میسازی و نابود میکنی، آسودهخاطر و در امان خواهد بود. | 13 |
kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
خداوند قوم برگزیدهٔ خود را ترک نخواهد کرد و ایشان را از یاد نخواهد برد. | 14 |
Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
بار دیگر داوری از روی عدل و انصاف اجرا خواهد شد و همهٔ درستکاران از آن پشتیبانی خواهند کرد. | 15 |
Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
کیست که به طرفداری از من برخیزد و در مقابل گناهکاران ایستادگی کند؟ چه کسی حاضر است با من علیه بدکاران بجنگد؟ | 16 |
Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
اگر خداوند مددکار من نمیبود بهزودی از بین میرفتم. | 17 |
Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
وقتی فریاد زدم که پاهایم میلغزند! تو، ای خداوند پر محبت، به فریادم رسیدی و دست مرا گرفتی. | 18 |
Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
هنگامی که فکرم ناراحت و دلم بیقرار است، ای خداوند، تو مرا دلداری میدهی و به من آسودگی خاطر میبخشی. | 19 |
Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
آیا حکمرانان شرور از حمایت تو برخوردار خواهند بود که به نام قانون هر نوع ظلمی را مرتکب میشوند؟ | 20 |
Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
آنها علیه درستکاران توطئه میچینند و بیگناهان را به مرگ محکوم میکنند. | 21 |
Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
اما خداوند صخره و پناهگاه من است و مرا از هر گزندی حفظ میکند. | 22 |
Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
خداوند، شریران و بدکاران را به سزای اعمالشان خواهد رسانید و آنها را از بین خواهد برد. آری، خداوند، خدای ما، ایشان را نابود خواهد کرد. | 23 |
Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.