< مزامیر 51 >

برای رهبر سرایندگان. مزمور داوود، دربارۀ زمانی که ناتان نبی پس از همبستر شدن داوود با بَتشِبَع، نزد او رفت. خدایا، بخاطر محبتت بر من رحم فرما. بخاطر رحمت بیکرانت گناهانم را محو کن. 1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
مرا از عصیانم کاملاً شستشو ده و مرا از گناهم پاک ساز. 2
Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
به عمل زشتی که مرتکب شده‌ام اعتراف می‌کنم؛ گناهم همیشه در نظر من است. 3
Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
به تو ای خداوند، بله، تنها به تو گناه کرده‌ام و آنچه را که در نظر تو بد است، انجام داده‌ام. حکم تو علیه من عادلانه است و در این داوری، تو مصون از خطا هستی. 4
Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
من از بدو تولد گناهکار بوده‌ام، بله، از لحظه‌ای که نطفهٔ من در رحم مادرم بسته شد آلوده به گناه بوده‌ام. 5
Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
تو از ما قلبی صادق و راست می‌خواهی؛ پس فکر مرا از حکمتت پُر ساز. 6
Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
گناه مرا از من دور کن تا پاک شوم؛ مرا شستشو ده تا سفیدتر از برف شوم. 7
Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
ای که مرا در هم کوبیده‌ای، شادی مرا به من بازگردان تا جان من بار دیگر مسرور شود. 8
Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
از گناهانم چشم بپوش و همهٔ خطاهایم را محو کن. 9
Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
خدایا، دلی پاک در درون من بیافرین و از نو، روحی راست به من عطا کن. 10
Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
مرا از حضور خود بیرون نکن و روح پاک خود را از من نگیر. 11
Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
شادی نجات از گناه را به من بازگردان و کمکم کن تا با میل و رغبت تو را اطاعت کنم. 12
Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
آنگاه احکام تو را به گناهکاران خواهم آموخت و آنان به سوی تو بازگشت خواهند نمود. 13
Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
ای خدایی که نجا‌ت‌دهندۀ من هستی، وجدان مرا از این گناه خونریزی پاک کن تا بتوانم در وصف عدالت تو سرود بخوانم. 14
Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
خداوندا، کمکم کن تا بتوانم دهانم را بگشایم و تو را ستایش کنم. 15
Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
تو از من قربانی حیوانی نخواستی، و گرنه آن را تقدیم می‌کردم. 16
Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
قربانی من این قلب شکسته و این روح توبه‌کار من است که به تو تقدیم می‌کنم؛ خدایا، می‌دانم که این هدیهٔ مرا خوار نخواهی شمرد. 17
Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
خدایا، به لطف خود صهیون را کامیاب ساز و دیوارهای اورشلیم را دوباره بنا کن. 18
Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
آنگاه بر مذبح تو گاوها ذبح خواهند شد و تو از انواع قربانیهایی که بر مذبح تو تقدیم می‌شوند خشنود خواهی گردید. 19
Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.

< مزامیر 51 >