< مزامیر 42 >
برای رهبر سرایندگان. قصیدۀ پسران قورَح. چنانکه آهو برای نهرهای آب اشتیاق دارد، همچنان ای خدا، جان من اشتیاق شدید برای تو دارد. | 1 |
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Maskil ne na’Ya’yan Kora maza. Kamar yadda barewa take marmarin ruwan rafuffuka, haka raina yake marmarinka, ya Allah.
آری، جان من تشنهٔ خداست، تشنهٔ خدای زنده! کی میتوانم به حضور او بروم و او را ستایش کنم؟ | 2 |
Raina yana ƙishin Allah, Allah mai rai. Yaushe zan tafi in sadu da Allah ne?
روز و شب گریه میکنم، و اشکهایم غذای من است؛ تمام روز دشمنان از من میپرسند: «پس خدای تو کجاست؟» | 3 |
Hawayena ne sun zama abincina dare da rana, yayinda mutane suke ce da ni dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
چون به گذشته فکر میکنم دلم میگیرد؛ به یاد میآورم که چگونه در روزهای عید، جماعت بزرگی را سرودخوانان و شادیکنان و حمدگویان به خانهٔ خدا هدایت میکردم! | 4 |
Waɗannan abubuwa ne nakan tuna sa’ad da nake faɗin abin da yake a raina, yadda dā nakan tafi tare da taron jama’a, ina bishe su a jere zuwa gidan Allah, da sowa ta farin ciki da kuma godiya a cikin taron biki.
ای جان من، چرا محزون و افسردهای؟ بر خدا امید داشته باش! او را دوباره ستایش کن، زیرا او خدا و نجاتدهندۀ توست! | 5 |
Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
در این دیار غربت دلم گرفته است، اما از این سرزمین اردن و کوههای حرمون و مصغر، تو را به یاد میآورم. | 6 |
Raina yana baƙin ciki a cikina; saboda haka zan tuna da kai daga ƙasar Urdun, a ƙwanƙolin Hermon, daga Dutsen Mizar.
خروش دریای متلاطم به گوشم میرسد، آنگاه که امواج و سیلابهای تو از سرم میگذرد. | 7 |
Zurfi kan kira zurfi cikin rurin matsirgar ruwanka; dukan raƙuma da igiyoyi sun sha kaina.
خداوندا، در طی روز مرا مورد لطف و رحمت خود قرار ده، تا هنگامی که شب فرا میرسد سرودی برای خواندن داشته باشم و نزد خدای حیات خود دعا کنم. | 8 |
Da rana Ubangiji yakan nuna ƙaunarsa, da dare waƙarsa tana tare da ni, addu’a ga Allah na raina.
به خدا که صخرهٔ من است میگویم: «چرا مرا فراموش کردهای؟ چرا باید به سبب ستم دشمنان نالهکنان به این سو و آن سو بروم؟» | 9 |
Na ce wa Allah Dutsena, “Me ya sa ka manta da ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?”
سرزنش دشمنانم مرا خرد کرده است، زیرا هر روز با کنایه به من میگویند: «پس خدای تو کجاست؟» | 10 |
Ƙasusuwana suna jin jiki da wahala yayinda maƙiyana suna mini ba’a, suna ce mini dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
ای جان من، چرا محزون و افسردهای؟ بر خدا امید داشته باش! او را دوباره ستایش کن، زیرا او خدا و نجاتدهندۀ توست! | 11 |
Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.