< مزامیر 147 >
خداوند را سپاس باد! چه نیکوست که خدای خود را با سرود بپرستیم؛ چه لذتبخش است که او را بستاییم! | 1 |
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
خداوند اورشلیم را دوباره بنا میکند و پراکندگان اسرائیل را جمع مینماید. | 2 |
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
او دلشکستگان را شفا میبخشد و زخمهای ایشان را میبندد. | 3 |
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
خداوند حساب ستارگان را دارد و نام هر یک از آنها را میداند. | 4 |
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
خداوند ما بزرگ و تواناست و حکمت او بیانتهاست. | 5 |
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
او فروتنان را سرافراز میکند، اما روی شریران را به خاک میمالد. | 6 |
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
خداوند را با سرودهای شکرگزاری بپرستید! او را با نغمهٔ بربط ستایش کنید! | 7 |
Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
او ابرها را بر آسمان میگستراند و باران را بر زمین میباراند و سبزه را بر کوهها میرویاند، | 8 |
Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
به حیوانات غذا میدهد و روزی جوجهکلاغها را میرساند. | 9 |
Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
خداوند به نیروی اسب رغبت ندارد و قدرت انسان او را خشنود نمیسازد؛ | 10 |
Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
خشنودی او از کسانی است که او را گرامی میدارند و به محبت وی امید بستهاند. | 11 |
Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
ای اورشلیم، خداوند را ستایش کن! ای صهیون، خدای خود را سپاس بگو! | 12 |
Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
زیرا او دروازههایت را محکم به روی دشمن بسته و فرزندانت را که در درون هستند برکت داده است. | 13 |
Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
او مرزهایت را در صلح و آرامش نگه میدارد و تو را با بهترین نان گندم سیر مینماید. | 14 |
Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
خداوند به زمین دستور میدهد و هر چه میفرماید بهسرعت عملی میشود. | 15 |
Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
او برف را مانند لحاف بر سطح زمین میگستراند و شبنم را همچون خاکستر همه جا پخش میکند. | 16 |
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
خداوند دانههای تگرگ را مانند سنگریزه فرو میریزد و کیست که تاب تحمل سرمای آن را داشته باشد؟ | 17 |
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
سپس دستور میدهد و یخها آب میشوند؛ باد میفرستد و آبها جاری میشوند. | 18 |
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
او کلام خود را به یعقوب بیان کرده است، و فرایض و قوانینش را به اسرائیل. | 19 |
Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
این کار را تنها در مورد اسرائیل انجام داده است و نه قوم دیگری؛ لذا قومهای دیگر با شریعت او آشنا نیستند. خداوند را سپاس باد! | 20 |
Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.