< مزامیر 135 >

سپاس بر خداوند! نام خداوند را بستایید! ای خدمتگزاران خداوند، او را نیایش کنید! 1
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
ای کسانی که در صحن خانهٔ خداوند می‌ایستید، او را پرستش نمایید! 2
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
خداوند را شکر کنید، زیرا او نیکوست. نام خداوند را بسرایید، زیرا نام او دلپسند است. 3
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
خداوند یعقوب را برای خود برگزید، و اسرائیل را تا قوم خاص او باشد. 4
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
می‌دانم که خداوند بزرگ است و از جمیع خدایان برتر! 5
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
او هر آنچه که بخواهد، در آسمان و زمین و حتی اعماق دریا، انجام می‌دهد. 6
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
ابرها را از جاهای دور دست زمین برمی‌آورد، رعد و برق و باد و باران ایجاد می‌کند. 7
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
خداوند پسران ارشد مصری‌ها را کشت و نخست‌زاده‌های حیواناتشان را هلاک کرد. 8
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
او بر ضد فرعون و قومش معجزات و علامات عظیم در مصر انجام داد. 9
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
ممالک بزرگ را مجازات کرد و پادشاهان مقتدر را از بین برد: 10
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
سیحون، پادشاه اموری‌ها و عوج، پادشاه باشان و همهٔ پادشاهان کنعان را، 11
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
و سرزمین آنها را همچون میراث به قوم خود اسرائیل بخشید. 12
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
ای خداوند، نام تو تا ابد باقی است! همهٔ نسلها تو را به یاد خواهند آورد. 13
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
تو قوم خود را داوری خواهی نمود و بر بندگان خود رحم خواهی کرد. 14
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
خدایان قومهای دیگر، بتهای ساخته شده از طلا و نقره هستند. 15
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
دهان دارند، ولی سخن نمی‌گویند؛ چشم دارند، اما نمی‌بینند؛ 16
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
گوش دارند، ولی نمی‌شنوند؛ حتی قادر نیستند نفس بکشند! 17
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
سازندگان و پرستندگان بتها نیز مانند آنها هستند. 18
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
ای بنی‌اسرائیل، خداوند را ستایش کنید! ای کاهنان، ای خاندان هارون، خداوند را ستایش کنید! 19
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
ای لاویان، خداوند را ستایش کنید! ای خداشناسان، او را ستایش کنید! 20
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
ای مردم اورشلیم، خداوند را ستایش کنید، زیرا او در اورشلیم ساکن است! سپاس بر خداوند! 21
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.

< مزامیر 135 >