< مزامیر 105 >

خداوند را شکر کنید و نام او را بخوانید؛ کارهای او را به تمام قومهای جهان اعلام نمایید. 1
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
در وصف او بسرایید و او را ستایش کنید؛ از کارهای شگفت‌انگیز او سخن بگویید. 2
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
ای جویندگان خداوند شادی نمایید و به نام مقدّس او فخر کنید! 3
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
خداوند و قوت او را طالب باشید و پیوسته حضور او را بخواهید. 4
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
عجایبی را که به عمل آورده است، به یاد آورید، و معجزات او و داوریهایی که صادر کرده است. 5
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
ای فرزندان خادم او ابراهیم، ای پسران یعقوب، که برگزیدۀ او هستید. 6
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
او خداوند، خدای ماست، و عدالتش در تمام دنیا نمایان است. 7
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
عهد او را همیشه به یاد داشته باشید، عهدی که با هزاران پشت بسته است؛ 8
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
عهد او را با ابراهیم، و وعدهٔ او را به اسحاق! 9
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
او با یعقوب عهد بست و به اسرائیل وعده‌ای جاودانی داد. 10
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
او گفت: «سرزمین کنعان را به شما می‌بخشم تا ملک و میراثتان باشد.» 11
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
بنی‌اسرائیل قومی کوچک بودند و در آن دیار غریب؛ 12
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
میان قومها سرگردان بودند و از مملکتی به مملکتی دیگر رانده می‌شدند. 13
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
اما خداوند نگذاشت کسی به آنها صدمه برساند، و به پادشاهان هشدار داد که بر ایشان ظلم نکنند: 14
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
«برگزیدگان مرا آزار ندهید! بر انبیای من دست ستم دراز نکنید!» 15
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
خداوند در کنعان خشکسالی پدید آورد و قحطی تمام سرزمین آنجا را فرا گرفت. 16
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
او پیش از آن یوسف را به مصر فرستاده بود. برادران یوسف او را همچون برده فروخته بودند. 17
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
پاهای یوسف را به زنجیر بستند و گردن او را در حلقهٔ آهنی گذاشتند. 18
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
او در زندان ماند تا زمانی که پیشگویی‌اش به وقوع پیوست، و کلام خدا درستی او را ثابت کرد. 19
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
آنگاه، فرعون دستور داد تا یوسف را از زندان بیرون آورده، آزاد سازند. 20
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
سپس او را ناظر خانهٔ خود و حاکم سرزمین مصر نمود 21
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
تا بر بزرگان مملکت فرمان راند و مشایخ را حکمت آموزد. 22
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
آنگاه یعقوب و فرزندانش به مصر، سرزمین حام، رفتند و در آن سرزمین ساکن شدند. 23
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
خداوند قوم خود را در آنجا بزرگ ساخت و آنها را از دشمنانشان قویتر کرد. 24
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
اما از طرف دیگر، خداوند کاری کرد که مصری‌ها بر قوم او ظلم کنند و ایشان را بردهٔ خود سازند. 25
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
سپس بندگان خود موسی و هارون را که برگزیده بود، نزد بنی‌اسرائیل فرستاد. 26
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
موسی و هارون، کارهای شگفت‌انگیز او را در میان مصری‌ها به ظهور آوردند، و معجزات او را در زمین حام. 27
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
خدا سرزمین مصر را با تاریکی پوشانید اما مصری‌ها فرمان خدا را مبنی بر آزاد سازی قوم اسرائیل اطاعت نکردند. 28
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
او آبهای ایشان را به خون مبدل ساخت و همهٔ ماهیانشان را کشت. 29
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
زمین آنها و حتی قصر فرعون پر از قورباغه شد. 30
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
به امر خداوند انبوه پشه و مگس در سراسر مصر پدید آمد. 31
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
به جای باران، تگرگ مرگبار و رعد و برق بر زمین مصر فرستاد 32
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
و باغهای انگور و تمام درختان انجیر مصری‌ها را از بین برد. 33
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
خداوند امر فرمود و ملخهای بی‌شماری پدید آمدند و تمام گیاهان و محصولات مصر را خوردند. 34
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
او همهٔ پسران ارشد مصری‌ها را کشت. 36
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
سرانجام بنی‌اسرائیل را در حالی که طلا و نقره فراوانی با خود برداشته بودند، صحیح و سالم از مصر بیرون آورد. 37
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
مصری‌ها از رفتن آنها شاد شدند، زیرا از ایشان ترسیده بودند. 38
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
خداوند در روز بر فراز قوم اسرائیل ابر می‌گسترانید تا آنها را از حرارت آفتاب محفوظ نگاه دارد و در شب، آتش به ایشان می‌بخشید تا به آنها روشنایی دهد. 39
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
آنها گوشت خواستند و خداوند برای ایشان بلدرچین فرستاد و آنها را با نان آسمانی سیر کرد. 40
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
او صخره را شکافت و از آن آب جاری شد و در صحرای خشک و سوزان مثل رودخانه روان گردید. 41
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
زیرا خداوند این وعدهٔ مقدّس را به خدمتگزار خویش ابراهیم داده بود که نسل او را برکت دهد. 42
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
پس او قوم برگزیدهٔ خود را در حالی که با شادی سرود می‌خواندند از مصر بیرون آورد، 43
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
و سرزمین قومهای دیگر را با تمام محصولاتشان به آنها بخشید 44
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
تا در آن سرزمین نسبت به وی وفادار مانده، از دستورهایش اطاعت نمایند. سپاس بر خداوند! 45
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< مزامیر 105 >