< مزامیر 103 >
مزمور داوود. ای جان من، خداوند را ستایش کن! ای تمام وجود من، نام مقدّس او را ستایش کن! | 1 |
Ta Dawuda. Yabi Ubangiji, ya raina; dukan abin da yake cikin cikina, yabi sunansa mai tsarki.
ای جان من، خداوند را ستایش کن و تمام مهربانیهای او را فراموش نکن! | 2 |
Yabi Ubangiji, ya raina, kada kuma ka manta dukan alheransa,
او تمام گناهانم را میآمرزد و همهٔ مرضهایم را شفا میبخشد. | 3 |
wanda yake gafarta dukan zunubai yake kuma warkar da dukan cututtuka,
جان مرا از مرگ میرهاند و با محبت و رحمت خود مرا برکت میدهد! | 4 |
wanda ya fanshi ranka daga rami ya naɗa maka rawani da ƙauna da kuma tausayi,
جان مرا با نعمتهای خوب سیر میکند تا همچون عقاب، جوان و قوی بمانم. | 5 |
Wanda ya ƙosar da kai da abubuwa masu kyau domin a sabunta ƙuruciyarka kamar na gaggafa.
خداوند عدالت را اجرا میکند و حق مظلومان را به آنها میدهد. | 6 |
Ubangiji yana aikata adalci da kuma gaskiya ga duk waɗanda aka danne.
او روشهای خود را بر موسی آشکار نمود و اعمال شگفتانگیز خود را به بنیاسرائیل نشان داد. | 7 |
Ya sanar da hanyoyinsa wa Musa, ayyukansa ga mutanen Isra’ila.
خداوند بخشنده و مهربان است؛ او دیر غضب و پر محبت میباشد. | 8 |
Ubangiji mai tausayi ne da kuma alheri, mai jinkirin fushi, cike da ƙauna.
خداوند همیشه توبیخ و تنبیه نمیکند و تا ابد خشمگین نمیماند. | 9 |
Ba zai yi ta zargi ba ba kuwa zai yi ta jin fushi har abada ba;
او با ما مطابق گناهانمان عمل ننموده و آنچنان که سزاوار بودهایم، ما را به سزای اعمالمان نرسانده است. | 10 |
ba ya yin da mu gwargwadon zunubanmu ko yă sāka mana bisa ga laifofinmu.
زیرا به اندازهای که آسمان از زمین بلندتر است، به همان اندازه محبت خداوند بر کسانی که او را گرامی میدارند عظیم میباشد! | 11 |
Gama kamar yadda sammai suke can bisa duniya, haka girmar ƙaunarsa yake wa masu tsoronsa;
به اندازهای که مشرق از مغرب دور است به همان اندازه خداوند گناهان ما را از ما دور کرده است! | 12 |
kamar yadda gabas yake daga yamma, haka ya cire laifofinmu daga gare mu.
همانطوری که یک پدر فرزندانش را دوست دارد، همچنان خداوند نیز کسانی را که او را گرامی میدارند دوست دارد. | 13 |
Kamar yadda mahaifi yake jin tausayin’ya’yansa, haka Ubangiji yake jin tausayin waɗanda suke tsoronsa;
خداوند از سرشت و فطرت ما آگاه است و میداند که خاک هستیم. | 14 |
gama ya san yadda aka yi mu, ya tuna cewa mu ƙura ne.
عمر انسان مانند علف و همچون گل صحرا میباشد، | 15 |
Game da mutum dai, kwanakinsa suna kamar ciyawa da suke haɓaka kamar fure a gona;
که روزی باد بر آن میوزد و از بین میرود و دیگر در آن مکانی که بوده، هرگز دیده نمیشود. | 16 |
iska kan hura a kansa sai ya ɓace ba a kuwa sāke tuna da inda dā yake.
اما محبت خداوند بر کسانی که او را گرامی میدارند، همیشگی است و او عدالت را در حق فرزندان آنانی که عهد و احکام او را حفظ میکنند، بجا میآورد. | 17 |
Amma daga madawwami zuwa madawwami ƙaunar Ubangiji tana tare da waɗanda suke tsoronsa, adalcinsa kuma tare da’ya’yansu,
tare da waɗanda suke kiyaye alkawarinsa suna kuma tuna su yi biyayya da farillansa.
خداوند تخت فرمانروایی خود را در آسمانها قرار داده است و از آنجا بر همهٔ موجودات حکمرانی میکند. | 19 |
Ubangiji ya kafa kursiyinsa a sama, masarautarsa kuwa na mulki a bisa duka.
ای همهٔ فرشتگان توانا که گوش به فرمان خداوند هستید تا دستورهایش را اجرا نمایید، او را ستایش کنید! | 20 |
Yabi Ubangiji, ku mala’ikunsa, ku jarumawa masu yi masa aiki, waɗanda suke yin biyayya da maganarsa.
ای همه لشکرهای آسمانی، ای خدمتگزاران خداوند، او را سپاس گویید! | 21 |
Yabi Ubangiji, dukanku rundunarsa ta sama, ku bayinsa waɗanda kuke aikata nufinsa.
ای همه مخلوقات خداوند، در هر جایی که هستید، او را بستایید! ای جان من، خداوند را ستایش کن! | 22 |
Yabi Ubangiji, dukanku ayyukansa ko’ina a mulkinsa. Yabi Ubangiji, ya raina.