< مزامیر 101 >

مزمور داوود. ای خداوند، محبت و عدالت تو را می‌ستایم و با سرود تو را می‌پرستم. 1
Ta Dawuda. Zabura ce. Zan rera wa ƙauna da adalcinka; gare ka, ya Ubangiji, zan rera yabo.
مراقب خواهم بود تا راه درست و بی‌عیب را در پیش بگیرم. نزد من کِی خواهی آمد؟ در خانه خود، با دلی راست زندگی خواهم کرد. 2
Zan yi hankali ga yin rayuwa marar zargi, yaushe za ka zo gare ni? Zan bi da sha’anin gidana da zuciya marar abin zargi
هر چیز بد و ناپسند را از پیش چشم خود دور خواهم نمود. کردار افراد نادرست را دوست نخواهم داشت و در کارهایشان سهیم نخواهم شد. 3
Ba zan kafa a gaban idanuna 1 wani abu marar kyau ba. Na ƙi jinin ayyukan mutane marasa aminci; ba za su manne mini ba.
نادرستی را از خود دور خواهم ساخت و با گناهکاران معاشرت نخواهم کرد. 4
Mutane masu mugun zuciya za su nesa da ni; ba abin da zai haɗa ni da mugunta.
کسی را که از دیگران بدگویی کند ساکت خواهم کرد؛ شخص مغرور و خودخواه را متحمل نخواهم شد. 5
Duk wanda ya yi ɓatanci wa maƙwabcinsa a ɓoye shi za a kashe; duk mai renin wayo da mai girman kai, ba zan jure masa ba.
من در پی اشخاص امین و خداشناس هستم تا آنها را به کاخ خود بیاورم. کسی که درستکار باشد، او را به کار خواهم گماشت. 6
Idanuna za su kasance a kan amintattu a cikin ƙasar, don su zauna tare da ni; tafiyarsa ba ta da zargi zai yi mini hidima.
حیله‌گر به کاخ من راه نخواهد یافت و دروغگو نزد من نخواهد ماند. 7
Babu mai ruɗun da zai zauna a gidana; babu mai ƙaryan da zai tsaya a gabana.
هر روز عده‌ای از شریران را نابود خواهم کرد تا شهر خدا را از وجود همهٔ آنها پاک سازم. 8
Kowace safiya zan rufe bakunan dukan mugaye a ƙasar; zan yanke kowane mai aikata mugunta daga birnin Ubangiji.

< مزامیر 101 >