< مزامیر 10 >
ای خداوند، چرا دور ایستادهای؟ چرا به هنگام سختیها خود را پنهان میکنی؟ | 1 |
Don me, ya Ubangiji, kake tsaya can da nesa? Me ya sa kake ɓoye kanka a lokutan wahala?
بیا و اشخاص متکبر و بدکار را که بر فقرا ظلم میکنند در دامهای خودشان گرفتار ساز. | 2 |
Cikin fariyarsa mugun mutum yakan cuci marasa ƙarfi, waɗanda yake kama cikin makircin da ya shirya.
آنها با غرور از مقاصد پلید خود سخن میرانند. آنها اشخاص طمعکار را میستایند ولی خدا را ناسزا میگویند. | 3 |
Yakan yi taƙama da ƙulle-ƙullen zuciyarsa; yana albarkaci mai haɗama yana kuma ƙin Ubangiji.
این بدکارانِ متکبر فکر میکنند خدایی وجود ندارد تا از آنها بازخواست کند. | 4 |
Cikin ɗaga kai mutum ba ya neman Allah; cikin tunaninsa ba ya ba da wata dama saboda Allah.
آنها در کارهایشان موفقند و دشمنانشان را به هیچ میشمارند و توجهی به احکام خدا ندارند. | 5 |
Hanyoyinsa kullum sukan yi nasara; yana da girman kai kuma dokokinka suna nesa da shi; yakan yi wa dukan abokan gābansa duban reni.
به خود میگویند: «همیشه موفق خواهیم بود و از هر مصیبتی به دور خواهیم ماند.» | 6 |
Yakan ce wa kansa, “Ba abin da zai girgiza ni; kullum zan yi murna ba zan taɓa shiga wahala ba.”
دهانشان آکنده از نفرین و دروغ و تهدید است و از زبانشان گناه و شرارت میبارد. | 7 |
Bakinsa ya cika da zage-zage da ƙarairayi da kuma barazana; wahala da mugunta suna a ƙarƙashin harshensa.
در روستاها به کمین مینشینند و اشخاص بیگناه را میکشند. | 8 |
Yakan yi kwanto kusa da ƙauyuka; daga kwanton yakan kashe marar laifi. Yana kallon waɗanda za su shiga hannunsa a ɓoye.
مانند شیر درنده، کمین میکنند و بر اشخاص فقیر و درمانده حمله میبرند و ایشان را در دام خود گرفتار میسازند. | 9 |
Yakan yi kwanto a ɓoye kamar zaki. Yakan yi kwanto don yă kama marasa ƙarfi; yakan kama marasa ƙarfi yă ja su cikin ragarsa.
اشخاص بیچاره در زیر ضربات بیرحمانهٔ آنها خرد میشوند. | 10 |
Yakan ragargaza waɗanda suka shiga hannu, su fāɗi; sukan fāɗi a ƙarƙashin ƙarfinsa.
این بدکاران در دل خود میگویند: «خدا روی خود را برگردانده و این چیزها را هرگز نمیبیند.» | 11 |
Yakan ce wa kansa, “Ai, Allah ya manta; ya rufe fuskarsa ba ya gani.”
ای خداوند، برخیز و این بدکاران را مجازات کن! ای خدا، بیچارگان را فراموش نکن! | 12 |
Ka tashi, Ubangiji! Ka hukunta miyagu, ya Allah. Kada ka manta da marasa ƙarfi.
چرا بدکاران به خدا ناسزا میگویند و مجازات نمیشوند؟ آنها در دل خود میگویند: «خدا از ما بازخواست نخواهد کرد»؟ | 13 |
Don me mugun mutum zai ƙi Allah? Don me yakan ce wa kansa, “Allah ba zai nemi hakki daga gare ni ba”?
اما ای خدا، تو میبینی! تو رنج و غم مردم را میبینی و به داد آنها میرسی. تو امید بیچارگان و مددکار یتیمان هستی. | 14 |
Amma kai, ya Allah, kana gani wahala da baƙin ciki; kana lura da yadda suke ɗaukansu a hannu. Marar taimako kan danƙa kansa gare ka; kai ne mai taimakon marayu
دست این بدکاران را بشکن. آنها را به سزای اعمالشان برسان و به ظلم آنها پایان بده. | 15 |
Ka karye hannun mugaye da kuma mugun mutum; ka nemi hakki daga gare shi saboda muguntar da ba za a gane ba.
خداوند تا ابد پادشاه است؛ قومهایی که او را نمیپرستند از سرزمین وی رانده و هلاک خواهند شد. | 16 |
Ubangiji Sarkin har abada abadin ne; al’ummai za su hallaka daga ƙasarsa.
ای خداوند، تو دعای بیچارگان را اجابت میکنی. تو به درد دل آنها گوش میدهی و به ایشان قوت قلب میبخشی. | 17 |
Kakan ji, ya Ubangiji sha’awar mai shan wahala; kakan ƙarfafa su, ka kuma saurari kukansu,
تو از حق یتیمان و مظلومان دفاع میکنی تا دیگر انسان خاکی نتواند آنها را بترساند. | 18 |
kana kāre marayu da waɗanda aka danne, domin mutum, wanda yake na duniya kada ƙara haddasa wata razana.