< امثال 1 >

امثال سلیمان، پادشاه اسرائیل، که پسر داوود بود: 1
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
این امثال به شما کمک خواهند کرد تا حکمت و ادب بیاموزید و بتوانید سخنان پرمغز را درک کنید. 2
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
آنها به شما یاد خواهند داد چگونه رفتار عاقلانه داشته باشید و با صداقت و عدالت و انصاف عمل کنید. 3
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
این امثال به جاهلان حکمت می‌بخشند و به جوانان فهم و بصیرت. 4
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
با شنیدن و درک این امثال، حتی دانایان داناتر می‌شوند و دانشمندان چاره اندیشی کسب می‌کنند تا بتوانند معانی گفتار پیچیدهٔ حکیمان را بفهمند. 5
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
ترس خداوند سرآغاز دانش است. کسی که حکمت و ادب را خوار می‌شمارد، جاهل است. 7
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
ای جوان، نصیحت پدرت را بشنو و از تعلیم مادرت رویگردان نشو، 8
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
زیرا سخنان ایشان مانند تاج و جواهر، سیرت تو را زیبا خواهند ساخت. 9
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
وقتی گناهکاران تو را وسوسه می‌کنند، تسلیم نشو. 10
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
اگر آنها به تو بگویند: «بیا در کمین مردم بنشینیم و آنها را بکشیم 11
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
و مانند قبر، آنها را ببلعیم و از هستی ساقط کنیم؛ (Sheol h7585) 12
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
از این راه ما اشیاء قیمتی فراوان به چنگ خواهیم آورد و خانه‌های خود را از این غنایم پر خواهیم ساخت؛ 13
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
هر چه به دست بیاوریم به تساوی بین خود تقسیم خواهیم کرد؛ پس بیا و با ما همدست شو!» 14
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
پسرم تو با آنها نرو و خود را از چنین افرادی دور نگه دار؛ 15
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
زیرا آنها همیشه در پی گناه و قتل هستند. 16
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
یک پرنده وقتی می‌بیند برایش دام گذاشته‌اند، از آن دوری می‌کند. 17
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
ولی این افراد چنین نیستند. آنها خودشان را به دام می‌اندازند و با دست خود گور خود را می‌کنند. 18
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
این است سرنوشت تمام کسانی که در پی سود نامشروع هستند. چنین اشخاص خود را نابود می‌کنند. 19
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
حکمت در کوچه‌ها ندا می‌دهد. 20
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
مردم را که در سر چهارراه‌ها و نزد دروازهٔ شهر جمع شده‌اند صدا کرده، می‌گوید: 21
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
«ای نادانان! تا کی می‌خواهید نادان بمانید؟ تا کی می‌خواهید دانایی را مسخره کنید و از آن متنفر باشید؟ 22
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
بیایید و مشورت مرا بپذیرید، و من روح خود را بر شما نازل خواهم کرد و شما را دانا خواهم ساخت. 23
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
«بارها شما را صدا کردم ولی توجه نکردید، التماس نمودم اما اعتنا ننمودید. 24
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
شما نصیحت و نکوهش مرا نپذیرفتید. 25
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
من نیز به مصیبت شما خواهم خندید، و هنگامی که بلا دامنگیرتان شود شما را مسخره خواهم کرد، 26
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
آری، وقتی بلا مانند طوفان شما را فرا گیرد و مصیبت مثل گردباد شما را احاطه کند، و سختی و بدبختی شما را از پای درآورد. 27
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
«هنگامی که آنها فریاد برآورند، به دادشان نخواهم رسید، و اگرچه با اشتیاق به دنبالم بگردند، مرا نخواهند یافت؛ 28
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
زیرا از دانایی متنفر بوده‌اند و از خداوند اطاعت نکرده‌اند. 29
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
نصیحت مرا گوش نگرفته‌اند و نکوهش مرا نپذیرفته‌اند. 30
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
بنابراین ثمرهٔ راهی را که در پیش گرفته‌اند خواهند دید. 31
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
زیرا سرکشی احمقان، ایشان را خواهد کشت و بی‌خیالی نادانان آنها را از پای در خواهد آورد. 32
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
ولی همهٔ کسانی که به من گوش دهند، از هیچ بلایی نخواهند ترسید و در امنیت زندگی خواهند کرد.» 33
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”

< امثال 1 >