< امثال 8 >

آیا ندای حکمت را نمی‌شنوید و به آواز بصیرت گوش نمی‌دهید؟ 1
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
حکمت دم دروازه‌های شهر و سر چهارراه‌ها و جلوی در هر خانه‌ای ایستاده، می‌گوید: 2
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
«ای مردم، شما را صدا می‌زنم. 4
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
ای انسانهای جاهل و نادان به ندای من گوش دهید و زیرکی و فهم کسب کنید. 5
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
به من گوش دهید، زیرا سخنان من گرانبهاست. من حقیقت و راستی را بیان می‌کنم و از ناراستی نفرت دارم. 6
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
سخنان من بر حق است و کسی را گمراه نمی‌کند. 8
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
سخنان من برای کسی که گوش شنوا داشته باشد واضح و روشن است. 9
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
تعلیمی که من می‌دهم از طلا و نقره گرانبهاتر است. 10
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
ارزش من از یاقوت بیشتر است و هیچ چیز را نمی‌توان با من مقایسه کرد. 11
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
«من حکمتم و از زیرکی و دانایی و بصیرت برخوردار می‌باشم. 12
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
اگر کسی خداترس باشد، از بدی نفرت خواهد داشت. من از غرور و تکبر، رفتار و گفتار نادرست متنفرم. 13
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
«منم که هدایت می‌کنم و فهم و بصیرت می‌بخشم. به نیروی من پادشاهان سلطنت می‌کنند و قضات به عدل و انصاف قضاوت می‌نمایند. 14
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
تمام رهبران و بزرگان جهان به کمک من حکمرانی می‌کنند. 16
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
«من کسانی را که مرا دوست دارند، دوست می‌دارم. آنانی که در جستجوی من باشند مرا خواهند یافت. 17
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
ثروت و حرمت، اموال و موفقیت در اختیار من است. 18
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
بخشش‌های من از طلای ناب و نقرهٔ خالص بهتر است. 19
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
راههای من عدل و حق است. 20
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
ثروت حقیقی از آن کسانی است که مرا دوست دارند، زیرا من خزانه‌های ایشان را پر می‌سازم. 21
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
«در ابتدا، قبل از آفرینش عالم هستی، خداوند مرا با خود داشت. 22
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
از ازل، پیش از به وجود آمدن جهان، من شکل گرفتم. 23
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
قبل از پیدایش اقیانوسها و چشمه‌های پر آب، 24
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
قبل از آنکه کوهها و تپه‌ها به وجود آیند، 25
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
قبل از آنکه خدا زمین و صحراها و حتی خاک را بیافریند من به وجود آمدم. 26
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
«هنگامی که خدا آسمان را استوار ساخت و افق را بر سطح آبها کشید من آنجا بودم. 27
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
وقتی ابرها را در آسمان گسترانید و چشمه‌ها را از اعماق جاری نمود، 28
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
وقتی حدود دریاها را تعیین کرد تا آبها از آن تجاوز نکنند و وقتی اساس زمین را بنیاد نهاد، 29
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
من نزد او معمار بودم. موجب شادی همیشگی او بودم و در حضورش شادی می‌کردم. 30
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
دنیا و انسانهایی که او آفریده بود مایهٔ خوشی من بودند. 31
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
«پس ای جوانان به من گوش دهید، زیرا همهٔ کسانی که از دستورهای من پیروی می‌کنند سعادتمندند. 32
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
به نصیحت من گوش کنید؛ عاقل باشید و نصیحت مرا رد نکنید. 33
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
خوشا به حال کسی که به من گوش دهد و هر روز جلوی در خانهٔ من انتظار مرا بکشد، 34
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
زیرا هر که مرا بیابد حیات را یافته و خداوند را خشنود ساخته است؛ 35
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
اما کسی که مرا از دست بدهد به جانش لطمه می‌زند، آنانی که از من متنفر باشند مرگ را دوست دارند.» 36
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”

< امثال 8 >