< امثال 2 >

ای پسرم، اگر به سخنانم گوش بدهی و دستورهای مرا اطاعت کنی، 1
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
به حکمت گوش فرا دهی و طالب دانایی باشی، 2
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
و اگر به دنبال فهم و بصیرت بگردی 3
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
و آن را مانند نقره و گنجهای پنهان بطلبی تا به چنگ آری، 4
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
آنگاه خدا را خواهی شناخت و اهمیت خداترسی را خواهی آموخت. 5
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
خداوند بخشندهٔ حکمت است و سخنان دهان او به انسان فهم و دانش می‌بخشد. 6
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
او به درستکاران حکمت می‌بخشد و از آنها محافظت می‌نماید. 7
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
او از اشخاص با انصاف و خداشناس حمایت می‌کند. 8
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
اگر به سخنانم گوش بدهی، خواهی فهمید که عدالت، انصاف و صداقت چیست و راه درست کدام است. 9
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
حکمت جزو وجود تو خواهد شد و دانش به تو لذت خواهد بخشید. 10
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
بصیرت و فهم تو، از تو محافظت خواهد کرد. 11
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
و تو را از افراد بدکار دور نگه خواهد داشت افرادی که سخنانشان انسان را منحرف می‌سازد، 12
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
افرادی که از راه راست برگشته‌اند و در ظلمت گناه زندگی می‌کنند، 13
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
افرادی که از کارهای نادرست لذت می‌برند و از کجروی و شرارت خرسند می‌شوند، 14
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
و هر کاری که انجام می‌دهند از روی حقه‌بازی و نادرستی است. 15
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
حکمت می‌تواند تو را از زنان بدکاره و سخنان فریبنده‌شان نجات دهد. 16
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
این گونه زنان، شوهران خود را رها نموده، پیمان مقدّس زناشویی را شکسته‌اند. 17
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
مردانی که به خانه‌های چنین زنانی قدم می‌گذارند، به سوی مرگ و نیستی پیش می‌روند و به مسیر حیات باز نمی‌گردند. 18
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
اما تو راه خداشناسان را پیش بگیر و از راه راست منحرف نشو، 20
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
زیرا درستکاران و خداشناسان در زمین زندگی خواهند کرد، 21
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
ولی بدکاران و خدانشناسان از زمین ریشه‌کن خواهند شد. 22
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.

< امثال 2 >